An fara watsa shirin talabijin na musamman mai kashi uku da ke da taken “Yiwu ta duniya –Yadda Xi Jinping ke kulawa da jagorantar ci gaban Yiwu” daga ranar 23 ga watan Yuli a tashar CCTV-1 ta babban rukunin gidajen rediyo da talibijin na kasar Sin (CMG).
Dauke da yadda babban sakataren kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin Xi Jinping ke kulawa da jagorantar ci gaban Yiwu a matsayin babban jigo, shirin ya ba da cikakken bayani kan yadda Yiwu ta zurfafa aiwatar da dabarar “Takwas-Takwas” (wato yin amfani da babban fifikon lardin a fannoni takwas, da daukar matakai takwas na raya lardin) dake jagorantar zamanantar da lardin Zhejiang a cikin shekaru 20 da suka gabata, tare da inganta ci gaban tattalin arzikin gundumomi mai inganci bisa yanayin da suke ciki. (Bilkisu Xin)














