A ranar 8 ga watan Yulin 2026, an gudanar da babban taron bayar da lambobin yabo na kasar Sin a fannin kimiyya da fasaha a birnin Beijing. A yayin taron, an karrama masanin kimiyya dan kasar Jamus, Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog, da lambar yabo ta hadin gwiwar kasa da kasa a fannin kimiyya da fasaha ta Jamhuriyar Jama’ar Sin ta shekarar 2025, wadda ita ce babbar lambar yabo ta kimiyya da kasar ke bai wa masana kimiyya na kasashen waje.
Herzog, kwararre a fannin fasahar kirkirarriyar basira ta AI, ya zo kasar Sin ne a shekarar 2014 bisa gayyatar da aka yi masa don ya jagoranci wani aiki na kirkira da ya kunshi fannoni daban-daban da zai sada tsarin birane da fasahar AI.
A wata hira ta musamman da ya yi da wakilin CMG kwanan nan, ya yi tsokacin cewa, kasar Sin ta tara dimbin kwararrun masu bincike na sahun farko, wadanda ya yi amannar cewa “za su kawo sauyi mai kyau.”
Kasancewar shi ganau ne ba jiyau ba dangane da turbar zamanantarwa ta kasar Sin, Herzog ya lura cewa, “Kasar Sin tana da tsari mai kyau na aiwatar da dabarun ci gaba, kuma a ganina, wannan shi ne abin da ya sa kasar ta zama ta daban da saura.” (Abdulrazaq Yahuza Jere)














