A ranar 23 ga watan Yulin nan, ofishin jakadancin Sin a Nijeriya ya shirya wani karamin taro a Abuja domin murnar cika shekaru 99 da kafuwar rundunar sojin ’yantar da jama’ar kasar Sin (PLA).
Taron ya samu halartar Yu Dunhai, jakadan Sin a Nijeriya, da Janar Christopher Gwabin Musa (mai ritaya), ministan tsaro na Nijeriya, da babban kanal Ouyang Haisheng, babban jami’in harkokin tsaro na ofishin jakadancin Sin, da kuma wasu manyan jami’ai daga hedikwatar rundunar sojin Nijeriya.
A cikin jawabinsa, jakada Yu ya bayyana cewa, karkashin jagorancin Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, rundunar sojin ’yantar da jama’ar kasar Sin (PLA) ta ba da gagarumar gudunmawa wajen ’yantar da jama’a, da samun ’yancin kai da kuma farfado da kasar, tare da zama tamkar babbar katangar karfe wacce take kare martabar yankunan kasa, da tsaro, da kuma muradun ci gaban kasar Sin.
Ya yi nuni da cewa, sojojin kasar Sin suna sauke nauyin da ke wuyar rundunar sojin babbar kasa a duniya a fagen sha’anin kasa da kasa, kana suna shiga cikin tafiyar da harkokin tsaron duniya yadda ya kamata, sannan suna ba da gudunmawa wajen kiyaye zaman lafiya a duniya. Kasar Sin a shirye take ta zurfafa hadin gwiwa da Nijeriya a fannin tsaro tare da magance dimbin kalubale irin su ta’addanci.
A cikin jawabinsa kuwa, minista Musa ya bayyana cewa dangantakar da ke tsakanin Sin da Nijeriya na samun ci gaba cikin nasara, kuma hadin gwiwar soji na tafiya a kan turba mai kyau. Ya kara da cewa, Sin abokiyar kawance ce ta hakika ga Nijeriya da sauran kasashen Afirka.
Nijeriya a shirye take ta ci gaba da hada hannu da Sin domin karfafa kwazonta na aiki da kuma inganta tsaro da samun wadata a matakin yanki. (Abdulrazaq Yahuza Jere)














