ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara

by Sulaiman
48 minutes ago
Dauda Lawal

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana aniyarsa ta dawo da masana’antar yadi da kuma bunƙasa noman auduga a jihar, bayan ziyarar da ya kai Yankin Masana’antu na Glo-Djigbe (GDIZ) da ke Jamhuriyar Benin tare da Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, da wasu gwamnoni.

Da yake jawabi bayan zagayen duba cibiyar masana’antun, Dauda Lawal ya ce abin da ya gani ya tuna masa da lokacin da masana’antar yadi ta Zamfara ke ɗaya daga cikin manyan hanyoyin samar da ayyukan yi da bunƙasa tattalin arzikin jihar.

Ya bayyana cewa, ya taso ne a cikin yanayin wannan masana’anta, yana mai cewa mahaifinsa na daga cikin masu mallakar Masana’antar Yadi ta Zamfara, wadda a lokacin take gudanar da aiki sau uku a rana, inda kowane rukuni ke ɗaukar ma’aikata kusan 2,000.

ADVERTISEMENT

Gwamnan ya ƙara da cewa, a wancan lokaci Zamfara na da masana’antun tace auduga guda 23 da kuma masana’antar sarrafa man auduga, inda har tsabar auduga ake sarrafawa zuwa man girki.

A cewarsa, nasarar da ya gani a yankin masana’antun na Glo-Djigbe ta ƙara masa ƙwarin gwiwa wajen dawo da sarkar darajar auduga gaba ɗaya, daga noma zuwa sarrafawa da kuma samar da kayayyakin yadi a Zamfara.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000 A Kaduna

Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki

“Wannan ziyara ta nuna min hanya a fili. Dawo da wannan masana’anta na ɗaya daga cikin abubuwan da nake son bari a matsayin gadon mulkina a Zamfara, kuma na ƙuduri aniyar tabbatar da hakan,” inji Lawal.

Ya bayyana cewa farfaɗo da masana’antar auduga da yadi ba wai kawai zai ƙarfafa manoma ba ne, har ma zai buɗe damammakin kasuwanci ga masu sarrafa kayayyaki da masana’antun cikin gida, tare da samar da dubban guraben aikin yi da inganta rayuwar al’ummar jihar.

Ziyarar ta kasance wani ɓangare na shirin Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na kafa cibiyoyin sarrafa kayayyakin noma a sassa daban-daban na Nijeriya domin bunƙasa masana’antu da ƙara darajar albarkatun ƙasa.

Dauda Lawal
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000 A Kaduna
  • Sulaiman
    Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin
  • Sulaiman
    Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba
  • Sulaiman
    An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

MASU ALAKA

Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000  A Kaduna
Manyan Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000 A Kaduna

July 26, 2026
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Rahotonni

Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki

July 25, 2026
Kungiya Ta Nemi Mambobinta Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani
Labarai

Kungiya Ta Nemi Mambobinta Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani

July 25, 2026

LABARAI MASU NASABA

Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara

Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara

July 26, 2026
Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000  A Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000 A Kaduna

July 26, 2026
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki

July 25, 2026
Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

July 25, 2026
Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

July 25, 2026
Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

July 25, 2026
Yadda Ake Faten Dankalin Turawa Da Kaza

Yadda Ake Faten Dankalin Turawa Da Kaza

July 25, 2026
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

July 25, 2026
Baya Ga “Sanyi Irin Na Sin”, Akwai Wasu Abubuwa Da Yawa Da Masu Yawon Bude Ido Na Turai Ke Sha’awa Kan Kasar

Baya Ga “Sanyi Irin Na Sin”, Akwai Wasu Abubuwa Da Yawa Da Masu Yawon Bude Ido Na Turai Ke Sha’awa Kan Kasar

July 25, 2026
Rodri Ya Amince da Tayin Komawa Real Madrid

Rodri Ya Amince da Tayin Komawa Real Madrid

July 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.