Jakadan Birtaniya mai barin gado a Nijeriya, Richard Montgomery, ya bayyana a ranar Talata cewa sauye-sauyen tattalin arzikin da Shugaba Bola Tinubu ya aiwatar za su sanya Nijeriya ta samu ingantacciyar makoma na tsawon lokaci.
Montgomery ya ce duk da cewa wadannan sauye-sauyen sun jawo wa talakawa wahalhalu na dan lokaci, suna da matukar muhimmanci wajen farfado da tattalin arzikin kasar.
Mai bai wa Shugaban Hukumar Tara Haraji ta Nijeriya (NRS) shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Dakta Zacch Adedeji, Dare Adekanmbi, ya bayyana cewa jakadan ya fadi hakan ne a Abuja yayin ziyarar ban kwana da ya kai Hedikwatar Hukumar Tara Haraji.
Jakadan ya ce: “Kasancewa a Nijeriya tsawon shekaru uku a lokacin da abubuwa masu kyau da dama suka faru abin burgewa ne kwarai.”
Ya ci gaba da cewa: “Na san cewa sauye-sauyen tattalin arziki suna da wahala, kuma suna iya jawo wa talakawa kuncin rayuwa na dan lokaci, kamar rage darajar kudi, hauhawar farashi da makamantansu.
“Amma ina ci gaba da bayyana wa gwamnatinmu, har da sabon Firayim Ministanmu, Andy Burnham, wanda ke fatan tattaunawa da Mai Girma Shugaba Bola Tinubu cikin makwanni masu zuwa, irin muhimmancin wadannan sauye-sauyen.
“Ko aikin da Yemi Cardoso ya yi a Babban Bankin Nijeriya (CBN), ko wanda Wale Edun ya fara a Ma’aikatar Kudi, da kuma aikin da kai (Zacch Adedeji) da Taiwo Oyedele, wanda yanzu shi ne Ministan Kudi kuma Ministan Daidaita Tattalin Arziki, kuka yi wajen gyaran tsarin haraji da tafiyar da harkokin kudaden gwamnati abin a yaba ne.
“Na san Nijeriya kasa ce mai sarkakiya. Na kuma san tsara kasafin kudi da tafiyar da kudaden gwamnati abu ne mai wahala saboda yadda tsarin kasafin kudi ke gudana a Majalisar Dokoki ta Kasa.
“Saboda haka, ina ganin abin da ministocin kudi da kai da tawagarka kuka yi wajen dora Nijeriya kan turba mai kyau da kuma inganta yadda ake tafiyar da kudaden gwamnati abin yabawa ne kwarai.
“Na yaba ba wai kawai da kwarewar fasaha ba, har ma da hikimar siyasa da tawagarku ta nuna wajen gudanar da wadannan sauye-sauyen.
A cikin shekara ukun nan, abin farin ciki ne ganin an samar da sabuwar tawaga a NNPCL, an jawo karin masu zuba jari, kuma kimar amincewar masu ba da bashi ga Nijeriya ta inganta.
“Ina ganin abin da ku da sauran manyan jami’an da ke tafiyar da tattalin arzikin kasa kuka yi yana da matukar muhimmanci ga makomar Nijeriya. Don haka ina matukar yaba muku.
“Na sha fada wa wasu manyan jami’ai cewa shekaru hudu masu zuwa ya kamata su mayar da hankali wajen daga bunkasar tattalin arziki daga kashi 4 zuwa kashi 7 cikin dari, domin wannan ne zai kawo sauyi ga rayuwar talakawa. Kuma ina da tabbacin cewa tare da gudummawarku da ta sauran masu ruwa da tsaki, hakan zai yiwu.”
Montgomery ya bayyana Hukumar Tara Haraji ta Nijeriya (NRS) a matsayin daya daga cikin mafi kyawun abokan huldar Birtaniya, tare da yabawa Adedeji kan yadda yake gudanar da aiki mai wahala amma mai amfani.
Haka kuma, ya yaba da hadin gwiwar da ke tsakanin NRS da Hukumar Tara Haraji ta Birtaniya (HMRC) wajen yin bitar tsarin aiki da musayar kwarewa.
A nasa jawabin, Shugaban NRS, Dakta Zacch Adedeji, ya ce abin takaici ne yadda Montgomery ke barin Nijeriya a wannan lokaci, tare da yabawa yadda ya gudanar da aikinsa.
Ya ce: “Yadda ka gudanar da wannan aiki ya sauya labari gaba daya, musamman irin goyon bayan da ka ba mu, na kai tsaye da kuma ta fuskar taimakon fasaha wajen aiwatar da sauye-sauyenmu.
“Wannan goyon baya ba zai taba gushewa daga zukatanmu ba. Ina kuma gode maka da jajircewarka da sadaukarwarka.
“Ko da yake kana barin Nijeriya, kana iya ganin wasu daga cikin kyawawan sakamakon wadannan sauye-sauyen.
“Ka dauke mu a matsayin wasu muhimmin bangarori na tsarin tattalin arzikin Nijeriya, kuma irin wadannan tattaunawa sun taimaka sosai wajen tsara sauye-sauyenmu.
“Na kuma yarda da abin da ka ce cewa ci gaba mai dorewa ba ya dogara da bayar da tallafi kawai, sai dai a kan kulla hadin gwiwa mai amfani. Ina da tabbacin cewa irin wannan kyakkyawar alaka za ta ci gaba da kasancewa tare da wanda zai gaje ka.”













