ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki

by Rabi'u Ali Indabawa
1 hour ago
Birtaniya

Jakadan Birtaniya mai barin gado a Nijeriya, Richard Montgomery, ya bayyana a ranar Talata cewa sauye-sauyen tattalin arzikin da Shugaba Bola Tinubu ya aiwatar za su sanya Nijeriya ta samu ingantacciyar makoma na tsawon lokaci.

Montgomery ya ce duk da cewa wadannan sauye-sauyen sun jawo wa talakawa wahalhalu na dan lokaci, suna da matukar muhimmanci wajen farfado da tattalin arzikin kasar.

Mai bai wa Shugaban Hukumar Tara Haraji ta Nijeriya (NRS) shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Dakta Zacch Adedeji, Dare Adekanmbi, ya bayyana cewa jakadan ya fadi hakan ne a Abuja yayin ziyarar ban kwana da ya kai Hedikwatar Hukumar Tara Haraji.

ADVERTISEMENT

Jakadan ya ce: “Kasancewa a Nijeriya tsawon shekaru uku a lokacin da abubuwa masu kyau da dama suka faru abin burgewa ne kwarai.”

Ya ci gaba da cewa: “Na san cewa sauye-sauyen tattalin arziki suna da wahala, kuma suna iya jawo wa talakawa kuncin rayuwa na dan lokaci, kamar rage darajar kudi, hauhawar farashi da makamantansu.

LABARAI MASU NASABA

Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

“Amma ina ci gaba da bayyana wa gwamnatinmu, har da sabon Firayim Ministanmu, Andy Burnham, wanda ke fatan tattaunawa da Mai Girma Shugaba Bola Tinubu cikin makwanni masu zuwa, irin muhimmancin wadannan sauye-sauyen.

“Ko aikin da Yemi Cardoso ya yi a Babban Bankin Nijeriya (CBN), ko wanda Wale Edun ya fara a Ma’aikatar Kudi, da kuma aikin da kai (Zacch Adedeji) da Taiwo Oyedele, wanda yanzu shi ne Ministan Kudi kuma Ministan Daidaita Tattalin Arziki, kuka yi wajen gyaran tsarin haraji da tafiyar da harkokin kudaden gwamnati abin a yaba ne.

“Na san Nijeriya kasa ce mai sarkakiya. Na kuma san tsara kasafin kudi da tafiyar da kudaden gwamnati abu ne mai wahala saboda yadda tsarin kasafin kudi ke gudana a Majalisar Dokoki ta Kasa.

“Saboda haka, ina ganin abin da ministocin kudi da kai da tawagarka kuka yi wajen dora Nijeriya kan turba mai kyau da kuma inganta yadda ake tafiyar da kudaden gwamnati abin yabawa ne kwarai.

“Na yaba ba wai kawai da kwarewar fasaha ba, har ma da hikimar siyasa da tawagarku ta nuna wajen gudanar da wadannan sauye-sauyen.

A cikin shekara ukun nan, abin farin ciki ne ganin an samar da sabuwar tawaga a NNPCL, an jawo karin masu zuba jari, kuma kimar amincewar masu ba da bashi ga Nijeriya ta inganta.

“Ina ganin abin da ku da sauran manyan jami’an da ke tafiyar da tattalin arzikin kasa kuka yi yana da matukar muhimmanci ga makomar Nijeriya. Don haka ina matukar yaba muku.

“Na sha fada wa wasu manyan jami’ai cewa shekaru hudu masu zuwa ya kamata su mayar da hankali wajen daga bunkasar tattalin arziki daga kashi 4 zuwa kashi 7 cikin dari, domin wannan ne zai kawo sauyi ga rayuwar talakawa. Kuma ina da tabbacin cewa tare da gudummawarku da ta sauran masu ruwa da tsaki, hakan zai yiwu.”

Montgomery ya bayyana Hukumar Tara Haraji ta Nijeriya (NRS) a matsayin daya daga cikin mafi kyawun abokan huldar Birtaniya, tare da yabawa Adedeji kan yadda yake gudanar da aiki mai wahala amma mai amfani.

Haka kuma, ya yaba da hadin gwiwar da ke tsakanin NRS da Hukumar Tara Haraji ta Birtaniya (HMRC) wajen yin bitar tsarin aiki da musayar kwarewa.

A nasa jawabin, Shugaban NRS, Dakta Zacch Adedeji, ya ce abin takaici ne yadda Montgomery ke barin Nijeriya a wannan lokaci, tare da yabawa yadda ya gudanar da aikinsa.

Ya ce: “Yadda ka gudanar da wannan aiki ya sauya labari gaba daya, musamman irin goyon bayan da ka ba mu, na kai tsaye da kuma ta fuskar taimakon fasaha wajen aiwatar da sauye-sauyenmu.

“Wannan goyon baya ba zai taba gushewa daga zukatanmu ba. Ina kuma gode maka da jajircewarka da sadaukarwarka.

“Ko da yake kana barin Nijeriya, kana iya ganin wasu daga cikin kyawawan sakamakon wadannan sauye-sauyen.

“Ka dauke mu a matsayin wasu muhimmin bangarori na tsarin tattalin arzikin Nijeriya, kuma irin wadannan tattaunawa sun taimaka sosai wajen tsara sauye-sauyenmu.

“Na kuma yarda da abin da ka ce cewa ci gaba mai dorewa ba ya dogara da bayar da tallafi kawai, sai dai a kan kulla hadin gwiwa mai amfani. Ina da tabbacin cewa irin wannan kyakkyawar alaka za ta ci gaba da kasancewa tare da wanda zai gaje ka.”

Birtaniya
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kungiya Ta Nemi Mambobinta Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe
Rahotonni

Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto

July 25, 2026
NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci
Rahotonni

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

July 24, 2026
Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna
Rahotonni

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

July 18, 2026

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki

July 25, 2026
Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

July 25, 2026
Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

July 25, 2026
Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

July 25, 2026
Yadda Ake Faten Dankalin Turawa Da Kaza

Yadda Ake Faten Dankalin Turawa Da Kaza

July 25, 2026
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

July 25, 2026
Baya Ga “Sanyi Irin Na Sin”, Akwai Wasu Abubuwa Da Yawa Da Masu Yawon Bude Ido Na Turai Ke Sha’awa Kan Kasar

Baya Ga “Sanyi Irin Na Sin”, Akwai Wasu Abubuwa Da Yawa Da Masu Yawon Bude Ido Na Turai Ke Sha’awa Kan Kasar

July 25, 2026
Rodri Ya Amince da Tayin Komawa Real Madrid

Rodri Ya Amince da Tayin Komawa Real Madrid

July 25, 2026
Ministan Harkokin Wajen Sin Wang Yi Ya Yi Kira A Karfafa Hadin Gwiwa Na Kut-Da-Kut A SCO Domin Gina Duniya Mai Damawa Da Mabambantan Bangarori

Ministan Harkokin Wajen Sin Wang Yi Ya Yi Kira A Karfafa Hadin Gwiwa Na Kut-Da-Kut A SCO Domin Gina Duniya Mai Damawa Da Mabambantan Bangarori

July 25, 2026
Kalolin Kitso Na Zamani: Yadda Ake Yin Fulani Style

Muhimmancin Kula Da Gashi Domin Lafiyarsa Da Kyawunsa

July 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.