• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Kafa Kyakkyawan Misali A Fannin Kare Hakkokin Bil Adama

by CGTN Hausa
2 years ago
sin

Ga duk mai bibiyar al’amuran yau da kullum dake gudana a matakin kasa da kasa, ya kwana da sanin cewa, kasar Sin ta sake samun gurbi a hukumar kare hakkin bil adama ta MDD, sakamakon zabenta da aka sake yi, yayin taron koli na MDD da ya gudana a ’yan kwanakin baya, kuma bisa hakan, za ta kasance cikin mambobin hukumar tun daga shekarar 2024 dake tafe har zuwa 2026.

Wannan ne karo na shida, da Sin din ke samun damar ba da gudummawa a wannan hukuma ta MDD, tun bayan kafuwarta a shekarar 2006. To ko mene ne ya sanya har yanzu ake damawa da kasar Sin a wannan hukuma mai muhimmanci?

  • Sin Ta Kadu Ta Yi Tir Da Kisan Jama’a Masu Tarin Yawa Sakamakon Hari Kan Asibiti A Gaza 
  • Yadda Kasar Sin Ke Ba Da Gudummawar Zamanintar Da Kasashen Duniya Cikin Shekaru 10 Masu Zuwa

Hakika dalilan suna da yawa, amma kadan daga cikinsu su ne gamsuwar da sassan kasa da kasa suka yi, da irin nasarorin da Sin din ta cimma a bangarorin kare hakkokin bil adama a cikin gida, da ma yadda take taka rawar gani wajen shiga hadin gwiwar kare hakkin bil adama a matakin kasa da kasa.

Sanin kowa ne cewa, a matsayinta na daya daga cikin kasashe mambobin farko na MDD, kuma mai kujerar dindindin a majalissar, har kullum kasar Sin na shiga dukkanin ayyukan da suka shafi kare hakkin bil adama, tana sauke nauyin tallafawa ayyukan da suka shafi hakan, kana tana goya baya ga tsarin jagoranci na kare hakkokin bil adama yadda ya kamata.

Har ila yau, duniya ta gamsu da yadda Sin din ke ingiza duk wasu matakai na samun ci gaban manufofin kare hakkin bil adama cikin lumana kuma a dukkanin matakai.

LABARAI MASU NASABA

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kaza lika, Sin na martaba ka’idojin MDD, da sauran kudurorin da sassan kasa da kasa suka amince da su game da kare hakkin bil adama, wanda hakan ya sanya ta zama abun koyi ga sauran sassan duniya a wannan fage.

A ganin kasar Sin, kare martabar al’umma shi ne babban jigo na tabbatar da hakkokin bil adama, wato dai farin cikin al’umma shi ne kan gaba, idan ana batun kare hakkin bil Adama.

Ko shakka babu, al’ummar kasar Sin na kara cin gajiya daga nasarorin kasarsu, kuma Sin na sanya bukatun jama’a gaban komai, tana goyon bayan duk wasu tsare-tsare na samar da ci gaban al’umma daga dukkanin fannoni, ta yadda duniya ke yabawa, da irin gudummawarta a bangaren kare hakkokin bil Adama. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka
Daga Birnin Sin

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
Next Post
Kaduna

Na Sha Alwashin Magance Talauci Da Kashi 80 Cikin 100 A Jihata - Gwamnan Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

November 8, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

November 8, 2025
An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.