• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Za Ta Taka Rawa A Harkokin Duniya Kamar Haka

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Za Ta Taka Rawa A Harkokin Duniya Kamar Haka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau Litinin aka rufe taron shekara-shekara na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin na bana, inda Xi Jinping, wanda aka sake zabarsa a matsayin shugaban kasar Sin a wajen taron, ya yi jawabi don bayyana ayyukan da za a mai da hankali a kansu cikin sabon wa’adin aikinsa. A cewarsa, kasar Sin za ta yi kokarin gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya ga daukacin bil-Adama, da samar da karin gudunmowa don tabbatar da zaman lafiya a duniya, da ci gaban kasashe daban daban.

Duk burikan da kasar Sin ta sanya a gaba suna da girma. Sai dai ta yaya kasar za ta iya cika su kamar yadda ta tsara?

Za mu iya duba matakan da kasar ta dauka a baya a wadannan fannoni.

Aikin gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya ga daukacin bil-Adama ya shafi yunkurin tabbatar da ci gaban kasashe daban daban na bai daya. A wannan fanni, kasar Sin ta dade tana taimakawa kasashe masu tasowa wajen raya tattalin arziki, da gina kayayyakin more rayuwa, gami da kyautata zaman rayuwar al’ummominsu.

Idan mun dauki dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC) a matsayin misali. Tun bayan da aka kafa dandalin a shekarar 2000, har zuwa yanzu, kamfanonin kasar Sin sun taimakawa kasashen Afirka a fannonin gina da inganta layin dogo da tsayinsu ya zarce kilomita dubu 10, da hanyoyin mota da tsawonsu ya kai kusan kilomita dubu 100, da gadojin da yawansu ya kusan kai dubu 1, da tashohin jiragen ruwa kusan dari 1, gami da dimbin asibitoci da makarantu, inda aka samar da sabbin guraben aikin yi fiye da miliyan 4.5 ga mazauna wuraren da batun ya shafa.

Labarai Masu Nasaba

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Ban da wannan kuma, zaman lafiya da kwanciyar hankali,shi ne tushen ci gaban tattalin arziki. Ganin haka ya sa sojojin kasar Sin suka kwashe dimbin shekaru suna kokarin wanzar da zaman lafiya a wasu kasashen dake nahiyar Afirka da suka hada da Mali, da Sudan ta Kudu, da dai sauransu, da ba da kariya ga jiragen ruwan dakon kayayyakin ciniki da suke bi ta mashigin teku na Aden, da yankin tekun dake dab da kasar Somaliya, da samar da tallafin likitanci, da kai dauki na gaggawa, ga kasashen da suke da bukata, da dai makamantansu.

Haka zalika, a kwanan baya, bisa shiga tsakani da kasar Sin ta yi, kasashen Saudiya da Iran sun yanke shawarar kawo karshen kiyayya da juna, da maido da huldar diplomasiyya tsakaninsu, lamarin da ya aza harsashi ga kokarin tabbatar da kwanciyar hankali a yankin gabas ta tsakiya. Inda kasar Sin maras nuna son kai, wadda ta ki karkata ga wani bangare, ko kuma kulla wani rukuni, ta cimma nasarar yin sulhu, da kasashen yamma suka gaza neman ganin hakan ya tabbata, ta hanyar tsara manyan tsare-tsare bisa ra’ayin kai, da yin shawarwari don daidaita matsaloli.

Ta haka muna iya ganin cewa, kasar Sin ta dade tana kokarin aiwatar da matakai daya bayan daya, don taimakawa daidaita al’amura a duniyarmu.

Sai dai mene ne ra’ayoyin sauran kasashe dangane da ayyukan da kasar Sin ta yi, da muka ambata a sama?

Don amsa wannan tambaya, za mu iya duba sakonnin da wasu shugabannin kasashen Afirka suka aikewa shugaba Xi Jinping don taya shi murnar samun karin wa’adin shugabancin kasar. Inda Wavel Ramkalawan, shugaban kasar Seychelles, ya ce, “Kasar Sin za ta ci gaba da taka muhimmiyar rawa a kokarin sake gina wani tsarin duniya mai tushen girmama ra’ayoyin bangarori daban daban, da daukaka zaman lafiya, da hadin kai.” A nasa bangare, shugaban kasar Eritrea, Isaias Afwerki, ya ce yana da imani kan cewar “kasar Sin za ta samar da muhimmiyar gudunmowa ga kokarin gina wani nagartaccen tsarin kasa da kasa da zai amfani bangarori daban daban”. Kana Abdel Fattah Abdelrahman al-Burhan, shugaban gwamnatin rikon kwarya na kasar Sudan, ya ce “ Kasar Sin za ta hada kai da abokanta a kokarin sauke nauyin dake bisa wuyansu na tabbatar da zaman lafiya da ci gaban kasashe daban daban a duniya, da gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makoma ta bai daya tare.”

Sai dai maganar da ta fi burge ni, ita ce wadda Patrice Guillaume Athanase Talon, shugaban kasar Benin, ya fada, yayin da yake hira da wakilin wani gidan telabijin na kasar Faransa a kwanan baya. Inda ko da yake an yi kokarin juya amsarsa, amma duk da haka, shugaban ya tsaya kan nuna yabo ga kasar ta Sin. A cewarsa, “kasar Sin ta kasance kasar da ba wanda zai iya kyale ta a duniya. Kana kasar tana ba ni kwarin gwiwa. A ganina, tsari na raya kasa na kasar Sin, da yadda take dogaro da kanta, da nagartacciyar dabararta a fannin mulki, za su karfafa gwiwar dukkan kasashen da suke fama da koma bayan tattalin arziki, saboda misalin kasar ta nuna cewa, duk wata kasa za ta iya samun ci gaban tattalin arziki.”

Rawar da kasar Sin ta dade tana takawa a duniya ita ce, kokarin wanzar da zaman lafiya, da neman ganin ci gaban kasashe daban daban, da hadin gwiwa da su don tabbatar da moriyar juna, gami da kokarin raya kanta, ta yadda za ta iya samar da fasahohi masu amfani ga sauran kasashe, da karfafa gwiwarsu, a kokarin da suke na neman samun ci gaba. Kuma kasar za ta ci gaba da kokarin taka wannan muhimmiyar rawa a nan gaba. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Magoya Bayan Tinubu Sun Gargadi Atiku Da Obi Kan Yi Wa Shari’a Katsalandan

Next Post

Ban Taba Ba Ministan Shari’a Da CBN Umarnin Su Ki Mutunta Hukuncin Kotun Koli Ba – Buhari

Related

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya
Daga Birnin Sin

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

16 hours ago
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

17 hours ago
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

18 hours ago
Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

19 hours ago
Sin Ta Yi Kira Da A Ci Gaba Da Himmatuwa Wajen Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Ci Gaba Da Himmatuwa Wajen Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

20 hours ago
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa
Daga Birnin Sin

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

2 days ago
Next Post
Sin

Ban Taba Ba Ministan Shari'a Da CBN Umarnin Su Ki Mutunta Hukuncin Kotun Koli Ba - Buhari

LABARAI MASU NASABA

Super Falcons Zasu Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Zasu Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.