ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Za Ta Taka Rawa A Harkokin Duniya Kamar Haka

by CMG Hausa
3 years ago
Sin

A yau Litinin aka rufe taron shekara-shekara na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin na bana, inda Xi Jinping, wanda aka sake zabarsa a matsayin shugaban kasar Sin a wajen taron, ya yi jawabi don bayyana ayyukan da za a mai da hankali a kansu cikin sabon wa’adin aikinsa. A cewarsa, kasar Sin za ta yi kokarin gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya ga daukacin bil-Adama, da samar da karin gudunmowa don tabbatar da zaman lafiya a duniya, da ci gaban kasashe daban daban.

Duk burikan da kasar Sin ta sanya a gaba suna da girma. Sai dai ta yaya kasar za ta iya cika su kamar yadda ta tsara?

Za mu iya duba matakan da kasar ta dauka a baya a wadannan fannoni.

ADVERTISEMENT

Aikin gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya ga daukacin bil-Adama ya shafi yunkurin tabbatar da ci gaban kasashe daban daban na bai daya. A wannan fanni, kasar Sin ta dade tana taimakawa kasashe masu tasowa wajen raya tattalin arziki, da gina kayayyakin more rayuwa, gami da kyautata zaman rayuwar al’ummominsu.

Idan mun dauki dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC) a matsayin misali. Tun bayan da aka kafa dandalin a shekarar 2000, har zuwa yanzu, kamfanonin kasar Sin sun taimakawa kasashen Afirka a fannonin gina da inganta layin dogo da tsayinsu ya zarce kilomita dubu 10, da hanyoyin mota da tsawonsu ya kai kusan kilomita dubu 100, da gadojin da yawansu ya kusan kai dubu 1, da tashohin jiragen ruwa kusan dari 1, gami da dimbin asibitoci da makarantu, inda aka samar da sabbin guraben aikin yi fiye da miliyan 4.5 ga mazauna wuraren da batun ya shafa.

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Ban da wannan kuma, zaman lafiya da kwanciyar hankali,shi ne tushen ci gaban tattalin arziki. Ganin haka ya sa sojojin kasar Sin suka kwashe dimbin shekaru suna kokarin wanzar da zaman lafiya a wasu kasashen dake nahiyar Afirka da suka hada da Mali, da Sudan ta Kudu, da dai sauransu, da ba da kariya ga jiragen ruwan dakon kayayyakin ciniki da suke bi ta mashigin teku na Aden, da yankin tekun dake dab da kasar Somaliya, da samar da tallafin likitanci, da kai dauki na gaggawa, ga kasashen da suke da bukata, da dai makamantansu.

Haka zalika, a kwanan baya, bisa shiga tsakani da kasar Sin ta yi, kasashen Saudiya da Iran sun yanke shawarar kawo karshen kiyayya da juna, da maido da huldar diplomasiyya tsakaninsu, lamarin da ya aza harsashi ga kokarin tabbatar da kwanciyar hankali a yankin gabas ta tsakiya. Inda kasar Sin maras nuna son kai, wadda ta ki karkata ga wani bangare, ko kuma kulla wani rukuni, ta cimma nasarar yin sulhu, da kasashen yamma suka gaza neman ganin hakan ya tabbata, ta hanyar tsara manyan tsare-tsare bisa ra’ayin kai, da yin shawarwari don daidaita matsaloli.

Ta haka muna iya ganin cewa, kasar Sin ta dade tana kokarin aiwatar da matakai daya bayan daya, don taimakawa daidaita al’amura a duniyarmu.

Sai dai mene ne ra’ayoyin sauran kasashe dangane da ayyukan da kasar Sin ta yi, da muka ambata a sama?

Don amsa wannan tambaya, za mu iya duba sakonnin da wasu shugabannin kasashen Afirka suka aikewa shugaba Xi Jinping don taya shi murnar samun karin wa’adin shugabancin kasar. Inda Wavel Ramkalawan, shugaban kasar Seychelles, ya ce, “Kasar Sin za ta ci gaba da taka muhimmiyar rawa a kokarin sake gina wani tsarin duniya mai tushen girmama ra’ayoyin bangarori daban daban, da daukaka zaman lafiya, da hadin kai.” A nasa bangare, shugaban kasar Eritrea, Isaias Afwerki, ya ce yana da imani kan cewar “kasar Sin za ta samar da muhimmiyar gudunmowa ga kokarin gina wani nagartaccen tsarin kasa da kasa da zai amfani bangarori daban daban”. Kana Abdel Fattah Abdelrahman al-Burhan, shugaban gwamnatin rikon kwarya na kasar Sudan, ya ce “ Kasar Sin za ta hada kai da abokanta a kokarin sauke nauyin dake bisa wuyansu na tabbatar da zaman lafiya da ci gaban kasashe daban daban a duniya, da gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makoma ta bai daya tare.”

Sai dai maganar da ta fi burge ni, ita ce wadda Patrice Guillaume Athanase Talon, shugaban kasar Benin, ya fada, yayin da yake hira da wakilin wani gidan telabijin na kasar Faransa a kwanan baya. Inda ko da yake an yi kokarin juya amsarsa, amma duk da haka, shugaban ya tsaya kan nuna yabo ga kasar ta Sin. A cewarsa, “kasar Sin ta kasance kasar da ba wanda zai iya kyale ta a duniya. Kana kasar tana ba ni kwarin gwiwa. A ganina, tsari na raya kasa na kasar Sin, da yadda take dogaro da kanta, da nagartacciyar dabararta a fannin mulki, za su karfafa gwiwar dukkan kasashen da suke fama da koma bayan tattalin arziki, saboda misalin kasar ta nuna cewa, duk wata kasa za ta iya samun ci gaban tattalin arziki.”

Rawar da kasar Sin ta dade tana takawa a duniya ita ce, kokarin wanzar da zaman lafiya, da neman ganin ci gaban kasashe daban daban, da hadin gwiwa da su don tabbatar da moriyar juna, gami da kokarin raya kanta, ta yadda za ta iya samar da fasahohi masu amfani ga sauran kasashe, da karfafa gwiwarsu, a kokarin da suke na neman samun ci gaba. Kuma kasar za ta ci gaba da kokarin taka wannan muhimmiyar rawa a nan gaba. (Bello Wang)

Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Next Post
Sin

Ban Taba Ba Ministan Shari'a Da CBN Umarnin Su Ki Mutunta Hukuncin Kotun Koli Ba - Buhari

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.