• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta Kashe Saurayinta Saboda Ya Hana Ta Kason Damfarar Da Suka Yi

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Labarai
0
Ta Kashe Saurayinta Saboda Ya Hana Ta Kason Damfarar Da Suka Yi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’an rundunar ‘yansanda a Jihar Imo sun kama wata mata ‘yar shekara 27 mai suna Oluchi Nzemechi bisa zarginta da daba wa saurayinta, Kelechi Nzemechi, wuka har lahira sakamakon wata rigima da ta kaure tsakaninsu a kan kin ba ta kasonta na kudin da suka yi damfara ta intanet.

Jami’in Hulda da Jama’a na Rundunar ‘Yansandan Jihar, Henry Okoye, wanda ya bayyana hakan ga manema labarai a Owerri a lokacin da yake gabatar da wacce ake zargin, ya ce Oluchi ta amsa laifin kashe saurayin nata ne kan kin ba ta kaso daga sama da kudin kasar Indonesiya miliyan 250 da suka damfari wani mutum dan kasar.

  • Dan Takarar Gwamnan Katsina A NNPP Ya Ba Da Tallafin Miliyan 50 Ga ‘Yan Gudun Hijira
  • CDD Ta Soki NBC Kan Cin Tarar Trust TV Da Wasu Miliyan 20

Da take bayar da labarin mummunan al’amarin, rundunar ‘yansandan ta bayyana cewa wacce ake zargin ta yi ikirarin cewa saurayin nata da ta kashe ya gabatar da ita ga wanda za su damfara har ta kai ga sun samu wadannan kudade, inda ta kara da cewa ta yi amfani da wuka a kicin wajen daba masa wuka bayan da suka yi zazzafar gardama.

“Rundunar ‘yansandan ta gudanar da bincike mai zurfi sun cafke wata budurwa ‘yar shekara 27 mai suna Oluchi Nzemechi da ke unguwar Uzoagba a Karamar Hukumar Ikeduru ta Jihar Imo da laifin daba wa abokin aikinta, Kelechi Nzemechi, mai shekaru 31 wuka wanda ya kai shi ga mutuwa.

“Yayin da take amsa tambaya, wacce ake zargin ta amsa laifinta, ta yarda cewa masoyinta ne ya yaudare ta inda ya jefa hanyar damfarar intanet mai suna ‘yahoo yahoo’.

Labarai Masu Nasaba

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

A ranar 02/06/2024, ta yi zazzafar husuma da shi saboda ya kasa ba ta wani kaso na kudin da ake zargin ta kai Rupiah Miliyan 250 da suka samu daga hannun wani da suka damfara a Indonesia, inda daga nan ne ta yi amfani da wukar kicin ta daba masa wuka a wani bangare na jikinsa,” in ji ‘yan sanda.

A lokacin da take zantawa da ‘yan jarida, Oluchi ta bayyana yadda ta yi kokarin wanke kanta daga kashe shi ta hanyar rubuta wasikar yaudara, “A kokarin da na ke na boye laifina, na yi gaggawar rubutawa a takarda; ‘Kana tunanin za ka ci kudina ka tafi haka, ni uwa ce ga samari, ina zuwa don neman matarka da yaronka har da danginka. Sai na dora takardar a kan gawar sannan na gudu daga gidan,” in ji ta.

Wacce ake zargin ta kuma bayyana cewa tana zaune da wanda ta kashe tun shekarar 2019 inda suka haifi yaro tare. ASP Okoye ya ce za a gurfanar da wacce ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin: Amurka Ta Sake Yada Karairayi Ta Hanyar Zargin Sin Da Tallafawa Rasha Da Makamai

Next Post

Xi Jinping: Ba Zan Ci Amanar Jama’a Ba

Related

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

3 hours ago
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya
Ra'ayi Riga

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

6 hours ago
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas
Labarai

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

8 hours ago
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

10 hours ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

12 hours ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

24 hours ago
Next Post
Xi Jinping: Ba Zan Ci Amanar Jama’a Ba

Xi Jinping: Ba Zan Ci Amanar Jama’a Ba

LABARAI MASU NASABA

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.