ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dan Takarar Gwamnan Katsina A NNPP Ya Ba Da Tallafin Miliyan 50 Ga ‘Yan Gudun Hijira

Ya Nemi A Dukufa Da Addu'o'in Kan Tsaron Jihar Katsina

by yahuzajere
4 years ago
Katsina

Engr. Nura Khalid

Dan takarar kujerar Gwamnan Jihar Katsina a karkashin Jam’iyyar NNPP, Engr Nura Khalil ya tallafa wa ‘yan gudun hijirar jihar da kudi Naira Miliyan 50 domin rage musu wahalhalun da suke sha.

Dama dai Engr. Nura Khalil ya kafa wata gidauniya mai suna Nurakhalil Foundation wadda mai dakinsa Hajiya Farida Barau take jagoranta. Gidauniyar ta fi karfin shekara goma (10) da kafuwa inda har kullum take aikin taimakon marayu da ‘yan gudun Hijra, da taimakawa ga matasa maza da mata wajen karatunsu.

Ganin yadda ‘yan gudun hijrar ke shan wahalhalu, babu wajen kwana mai kyau sannan ga barazanar yunwa ta har sai sun fita sun yi barar abin da za su ci da iyalansu, wasu ma sun fadi cewa sai an yi fasikanci da su ake ba su abin da za su kai ma iyalansu, ya sa Engr Nura Khalil ya ware Naira Miliyan Hamsin (50,000,000) domin ganin ‘yan hijirar sun wadatu da abinci da tufafi.

ADVERTISEMENT

A zantawarsa da aka yi da shi, Khlalil ya bayyana cewa idan har mutum zai iya mika kudinsa ya sayi form din takara to shi a nashi tunanin gara ya taimaka ma wadannan bayin Allah da iftila’i ya fadama wa, “kana ji kana gani a raba ka da gidanka, wasu an kashe su, wasu kuma an sace su har yau babu labarinsu.” Ya bayyana.

  • Jerin Sunayen Sabbin Ministocin Da Buhari Ya Aike Wa Majalisar Dattijai Ta Tantance Su

Ya jajanta ma al’ummar Jihar Katsina baki dayan su a kan fargaba da har kullum suke kwana suke tashi da shi a zukatansu. Kana ya ba da shawarar kowa ya dukufa ga yin addu’a ba dare babu rana har Allah ya kawo ma Jihar Katsina sauki.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

  • https://leadership.ng/bandits-attack-katsina-communities-shoot-kidnap-scores/

Tuni dai kwamitin da aka kafa domin raba tallafin ya dukufa gudanar da aikin tsara rabon inda ake sa ran ‘yan gudun hijira na sassa daban-daban na Jihar Katsina su amfana.

 

 

 

katsina
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
Next Post
Sanatocin APC 3 Sun Sauya Sheka Zuwa PDP da NNPP

Sanatocin APC 3 Sun Sauya Sheka Zuwa PDP da NNPP

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.