• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tallafi: ‘Yan Kasuwa Dubu 10 Sun Samu Tallafin Dubu 50 Kowane A Adamawa

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
Adamawa

Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya cika alkawarin tallafawa masu kananan sana’o’i dubu 10, da Naira 50,000 kowanensu, da nufin bunkasa harkokin kasuwancinsu a sassan jihar.

Fintiri, ya bayyana haka a taro da masu kananan sana’o’in a dandalin taro na Mahmud Ribadu da ke Yola, ranar Juma’a.

  • Kasar Sin Ta Gano Filin Hakar Mai Na Farko A Ruwa Mai Zurfi Mai Yawan Ton Miliyan 100
  • Rikita-rikitar Sauka Da Komawar Sheikh Daurawa Shugabancin Hisbar Jihar Kano

Ya ce shirin na karfafawa da aka yi wa lakabin ‘yan kasuwan Fintiri’ muhimman ci gaba ne a yunkurin gwamnatoci na daukaka martabar zamantakewa da tattalin arzikin al’umma da ya hada duk bangarorin tattalin arziki.

M

Ya ci gaba da cewa “A matsayin gwamnati ta fahimci cewa kananan sana’o’i su ne kashin bayan al’ummomin yanki, da samar da sabbin abubuwa, samar da ayyukan yi, da kuma bayar da gudunmawar ci gaban jama’a da jiha.

LABARAI MASU NASABA

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

“Shawarar raba wadannan kudade ya samo asali ne daga jajircewar da aka nuna na kawar da talauci da kuma bai wa ‘yan kasuwa damar bunkasa a kasuwannin hada-hadar kudade.

“Mun yi amanna ta hanyar bada taimakon kudi kai tsaye ga masu kananan kasuwanci dubu 10, muna da niyyar habaka kudirinsu, habaka ayyukansu, da ba su damar habaka ayyukansu zuwa ga samun ci gaba.

“Na fahimci kalubalen da masu kananan sana’o’i ke fuskanta, kama daga rashin isasshen jari zuwa karancin kayan aiki da ababen more rayuwa, da irin wadannan tallafin kudi ba kawai na hannu ba ne, a’a dabarun saka hannun jari a Jihar Adamawa,” in ji gwamnan.

Da yake magana kan mutanen da suka amfana da shirin, gwamna Umaru Fintiri, ya bukaci da su yi amfani da kudaden yadda ya kamata, ya ce su zuba jari a cikin sana’o’insu, tare da yin amfani da damar da ke gabansu, samar da kirkire-kirkire, kere-kere, da ya ce nasarar da su ka samu na da nasaba da ci gaban jihar.

Shi ma da yake jawabi, kwamishinan ma’aikatar bunkasa harkokin kasuwanci ta jihar, Honarabul James Iliya, ya ce shirin ‘yan kasuwan Fintiri ya taba duk wani lungu da sako na al’ummar jihar, ya yaba wa gwamnan bisa cika alkawarin da ya yi a yakin neman zabe.

Tun da farko da take jawabi shugabar hukumar PAWECA, Hajiya Aisha Bawa Bello, ta bayyana wadanda suka ci gajiyar shirin a matsayin ‘yan kasuwa, ta kuma yaba wa gwamnan bisa irin damar da ya ba su, da ba kasafai ake samu ba na yi wa al’umma hidima.

Ta ce an zabo wadanda suka ci gajiyar tallafin dubu 10 ne daga sassa 226 na jihar, ta kuma bayyana wasu nasarorin da gwamnan ya samu tare da yin kira ga wadanda suka amfana da su mayar da hankali wajen sanin ya kamata da aiki tukuru.

Da ta ke magana a madadin wadanda su ka ci gajiyar shirin, Eunice Kiliyobas ta bayyana gwamna Fintiri a matsayin wanda ya kuduri aniyar bai wa mabukata dama, ta ce za su yi amfani da tallafin bisa hanyar da ta dace.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi
Kotu Da Ɗansanda

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
Manyan Labarai

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP
Labarai

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Next Post
Yadda Rayuwata Ta Sauya Bayan Mayar Da Tsintuwar Naira Miliyan 15 – Auwalu

Yadda Rayuwata Ta Sauya Bayan Mayar Da Tsintuwar Naira Miliyan 15 – Auwalu

LABARAI MASU NASABA

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.