• English
  • Business News
Friday, October 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tallafi: ‘Yan Kasuwa Dubu 10 Sun Samu Tallafin Dubu 50 Kowane A Adamawa

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
Adamawa

Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya cika alkawarin tallafawa masu kananan sana’o’i dubu 10, da Naira 50,000 kowanensu, da nufin bunkasa harkokin kasuwancinsu a sassan jihar.

Fintiri, ya bayyana haka a taro da masu kananan sana’o’in a dandalin taro na Mahmud Ribadu da ke Yola, ranar Juma’a.

  • Kasar Sin Ta Gano Filin Hakar Mai Na Farko A Ruwa Mai Zurfi Mai Yawan Ton Miliyan 100
  • Rikita-rikitar Sauka Da Komawar Sheikh Daurawa Shugabancin Hisbar Jihar Kano

Ya ce shirin na karfafawa da aka yi wa lakabin ‘yan kasuwan Fintiri’ muhimman ci gaba ne a yunkurin gwamnatoci na daukaka martabar zamantakewa da tattalin arzikin al’umma da ya hada duk bangarorin tattalin arziki.

M

Ya ci gaba da cewa “A matsayin gwamnati ta fahimci cewa kananan sana’o’i su ne kashin bayan al’ummomin yanki, da samar da sabbin abubuwa, samar da ayyukan yi, da kuma bayar da gudunmawar ci gaban jama’a da jiha.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

“Shawarar raba wadannan kudade ya samo asali ne daga jajircewar da aka nuna na kawar da talauci da kuma bai wa ‘yan kasuwa damar bunkasa a kasuwannin hada-hadar kudade.

“Mun yi amanna ta hanyar bada taimakon kudi kai tsaye ga masu kananan kasuwanci dubu 10, muna da niyyar habaka kudirinsu, habaka ayyukansu, da ba su damar habaka ayyukansu zuwa ga samun ci gaba.

“Na fahimci kalubalen da masu kananan sana’o’i ke fuskanta, kama daga rashin isasshen jari zuwa karancin kayan aiki da ababen more rayuwa, da irin wadannan tallafin kudi ba kawai na hannu ba ne, a’a dabarun saka hannun jari a Jihar Adamawa,” in ji gwamnan.

Da yake magana kan mutanen da suka amfana da shirin, gwamna Umaru Fintiri, ya bukaci da su yi amfani da kudaden yadda ya kamata, ya ce su zuba jari a cikin sana’o’insu, tare da yin amfani da damar da ke gabansu, samar da kirkire-kirkire, kere-kere, da ya ce nasarar da su ka samu na da nasaba da ci gaban jihar.

Shi ma da yake jawabi, kwamishinan ma’aikatar bunkasa harkokin kasuwanci ta jihar, Honarabul James Iliya, ya ce shirin ‘yan kasuwan Fintiri ya taba duk wani lungu da sako na al’ummar jihar, ya yaba wa gwamnan bisa cika alkawarin da ya yi a yakin neman zabe.

Tun da farko da take jawabi shugabar hukumar PAWECA, Hajiya Aisha Bawa Bello, ta bayyana wadanda suka ci gajiyar shirin a matsayin ‘yan kasuwa, ta kuma yaba wa gwamnan bisa irin damar da ya ba su, da ba kasafai ake samu ba na yi wa al’umma hidima.

Ta ce an zabo wadanda suka ci gajiyar tallafin dubu 10 ne daga sassa 226 na jihar, ta kuma bayyana wasu nasarorin da gwamnan ya samu tare da yin kira ga wadanda suka amfana da su mayar da hankali wajen sanin ya kamata da aiki tukuru.

Da ta ke magana a madadin wadanda su ka ci gajiyar shirin, Eunice Kiliyobas ta bayyana gwamna Fintiri a matsayin wanda ya kuduri aniyar bai wa mabukata dama, ta ce za su yi amfani da tallafin bisa hanyar da ta dace.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

October 23, 2025
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata
Ra'ayi Riga

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara
Labarai

Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

October 23, 2025
Next Post
Yadda Rayuwata Ta Sauya Bayan Mayar Da Tsintuwar Naira Miliyan 15 – Auwalu

Yadda Rayuwata Ta Sauya Bayan Mayar Da Tsintuwar Naira Miliyan 15 – Auwalu

LABARAI MASU NASABA

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

October 23, 2025
Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

October 23, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

October 23, 2025
Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

October 23, 2025
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

October 23, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kasar Sin Ta Karyata Rahoto Na Zuki-ta-malle Da Wata Cibiyar Binciken Amurka Ta Fitar Game Da Hadin Gwiwar Sin Da Yammacin Afirka

October 23, 2025
An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

October 23, 2025
Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 23, 2025
Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

October 23, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.