ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Alhaji Isa Kaita Wazirin Katsina (3)

by Idris Aliyu Daudawa and Sulaiman
3 weeks ago
Isa kaita

A shekarar 1968 ne, aka nada Alhaji Isa Kaita, shugaban Hukumar daukar ma’aikata ta Jihar Arewa ta tsakiya a zamanin Gwamnan Jihar Birgediya Abba Kyari ne, bugu da kari ya rike mukamin har zuwa watan Agusta na shekarar 1975. Daga 1 shekarar 1975 zuwa1977, Alhaji Isa Kaita, shi ne shugaban Hukumar Gidaje ta Jihar Kaduna. Ya yi tafiye- tafiyen aiki zuwa kusan dukkan kasashen Afrika, Turai, Amurka, Australiya, Asiya, da kuma New Zealand. Ya yo wakilci a Hukumar Alhazai ta kasa, a matsayin wakilin majalisar koli ta kula da harkokin Addinin Musulunci daga watan Agusta na shekarar 1978 zuwa watan Mayu na 1981. Har ila yau shi ne ma’ajin majalisar koli ta harkokin Addinin Musulunci daga shekarar 1977, har zuwa lokacin da ya rasu.

Ya kuma rike mukamai da dama da suka hada da-:

Ya zama mai bada shawara ga Bankin UBA na Nijeriya daga 1972 zuwa1972.

ADVERTISEMENT

Ya zama Darekta na Bankin Indiya, wanda daga baya kuma sai Allied Bank dag shekarar 1972-1972. Ya zama Darektan Bankin Union Dominion daga shekarar 1972 zuwa1975 ,Ya yi Darektan Kamfanin U. A. C.

Darekta na kamfanin Kayce Challrams, Safa Foam Abbot, Songhai, Kuma shi ne shugaban Hukumar harshen Hausa tun daga shekarar1 960.

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Gambo Sawaba (1)

Tarihin Alhaji Isa Kaita Wazirin Katsina (2)

Alhaji Isa Kaita, mutum ne mai kaunar karance-karance, da wasanni. A sha’anin wasanni, shi ne shugaban kulob din kwallon kafa na Dawaki na Kaduna tun daga 1960 zuwa har lokacn da ya bar duniya, shi ne shugaban kulob na Sukuwar Dawaki ta Kaduna tun daga 1958, har zuwa shekarar da ya rasu, shi ne Uban kulob din da ake kira da suna Crocodile daga 1970, har zuwa lokacin daya rasu, ya zama wakili a Rotary club na Kaduna. Yana dda cikin iyayen kungiyar wasan fibes na Kaduna da aka nada a shekarar 1968.

A shekarar 1980 ce tsohon Shugaban kasar Nijeriya, Alhaji She Usman Aliyu Shagari, ya nada shi shugaban Hukumar kula da da’ar ma’aikata, majalisar dattijai haka ta amince da nadin na sa. A ranar 16 ga watan Yuli na shekarar1981 ne Shugaban kasa ya rantsar da shi kan shi mukamin. Bayan juyin mulkin na ranar 31 ga watan Disamba na 1983 ne, Alhaji Isa Kaita ya koma Kaduna a watan janairu na 1984, bayan da aka rushe Hukumar kula da da’ar ma’aikatan ranar 5 ga Janairu 1984. Allah ya kawo karshen rayuwar Alhaji Isa Kaita ranar 26 ga watan Nuwamba 1994, bayan da ya yi fama da jinyai muna addu’ar Allah ya jikansa da kuma Rahamsheshi.

Wannan shi ne karshen tarihin Alhaji Isa Kaita Wazirin Katsina mako mai zuwa da yardar Allah za mu kawo maku wani tarihi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tarihin Gambo Sawaba (1)
Tarihi

Tarihin Gambo Sawaba (1)

December 7, 2025
Tarihin Alhaji Isa Kaita Wazirin Katsina (2)
Tarihi

Tarihin Alhaji Isa Kaita Wazirin Katsina (2)

November 22, 2025
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Next Post
Xi Ya Jaddada Muhimmancin Inganta Hanyoyin Kula Da Tafiyar Da Intanet Na Dogon Zango

Xi Ya Jaddada Muhimmancin Inganta Hanyoyin Kula Da Tafiyar Da Intanet Na Dogon Zango

LABARAI MASU NASABA

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.