ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Gambo Sawaba (1)

by Idris Aliyu Daudawa
6 months ago
Sawaba

An haifi Hajiya Hajaratu Gambo Sawaba a shekarar 1933 a birnin Zariya, Jihar Kaduna. Sunan Mahaifinta, Isaac Dakwada, wanda shi ɗan asalin ƙasar Ghana ne, yayin da kuma ita  mahaifiyarta da ake kira da suna Fatima ta fito ne daga cikin kabilar Nupawa. Yarintarta ko nace ƙuruciyarta ta cika da nauyin da ya  fara yi mata yawa tun da wuri, bayan rasuwar mahaifinta tana ƙarama, sannan kuma da mutuwar mahaifiyarta ba da jimawa ba.

Tun tana yarinya, Hajiya Gambo wadda ta saba da yin gwagwarmaya, inda ta nuna ƙarfin hali da kuma nuna shi ’yanci wani abu ne mai daɗi. Ta yi karatu a ne a Makarantar Natiɓe Authority da ke Tudun Wada, Zariya, amma iliminta ya tsaya ne bakin iyakar Firamare  a sanadiyar auren da aka yi mata tun tana kusan ‘yar shekara 13—wannan kuma  a wancan lokacin wani abu da ya zama ruwan dare game duniya a Arewacin Nijeriya. Ko da yake auren da tayi bai daɗe ba, wannan ne ya buɗe mata ido kan buƙatar cewa mata suna da ’yancin  su yi zaɓe kai har ma suna iya zama wakilan al’umma a majalisu, wannan kuma ta ɓangaren harkar siyasa ne.

  • Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar
  • Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

Rayuwarta ta sirri ta shahara da aure-aure masu yawa inda har sai da  ta yi aure har sau  biyar baki ɗaya inda  kuma mijinta na huɗu, ana kiransa da suna Abubakar. Duk da cewa aurarrakain da ta yi sun kasance da manyan matsaloli na ƙalubale, ita ce ta ke ɗaukar gabarar ɗawainiyarsu data tafiyar da gida, haka ta haɗa abin ga kulawa da gida, ta waje ɗaya ga kuma lamarin  gwagwarmayar siyasa  wadda a wancan lokacin tana da matuƙar haɗari.

ADVERTISEMENT

Gambo Sawaba ta shiga siyasa tun tana  matashiya, inda ta  zama ‘yar jam’iyyar Northern Elements Progressiɓe Union wato (NEPU), jam’iyyar marigayi Malam Aminu Kano, wadda daga baya kuma aka sauaya mata suna zuwa PRP People’s Redemption Party  babbar  jam’iyyar adawa ce d take da mai tsattsauran ra’ayi, da take  ƙalubalantar waɗanda suke da mulki a hannunsu bama a Arewa kaɗai ba sai da ta mulki Nijeriya  Jam’iyyar NPC Jam’iyyar su Abubakar Tabawa Balewa Ahmadu Bello Sardauna Sakkwato da dai sauran  manyan ƴan siyasa. Ta kasance ɗaya daga cikin muryoyin mata da suka fi ƙarfi  a  cikin jam’iyyar, tana yaɗa manufofin bai wa mata ’yancin yin zaɓe, shiga siyasa, ilimi da kuma kariya daga wasu  munanan al’adun da basu zama dole sai an yi su ba.

Gwagwarmayar  da take yi ne bayan data  fito  a filihakan yasa ta  samu girmamawar manyan Shugabanni na ƙasa, ciki har da jagoran siyasar Kudu maso gabashin Nijeriya Dakta Nnamdi Azikiwe, wanda ake cewa shi ne ya  kira da  sunan mai laƙabin “Sawaba”—abinda yake nufin ’yanci a kalmar Hausa.

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

Sawaba
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

MASU ALAKA

Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Tarihi

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

May 30, 2026
Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya
Tarihi

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

February 22, 2026
Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959
Tarihi

Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959. (2)

January 11, 2026
Next Post
Matsalar Rashin Yarda Tsakanin Ma’aurata

Matsalar Rashin Yarda Tsakanin Ma’aurata

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.