ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Alhaji Isa Kaita Wazirin Katsina (2)

by Idris Aliyu Daudawa and Sulaiman
6 months ago
Isa kaita

… ci gaba daga makon da ya gabata.

Bugu da kari ma ya halarci bikin nadin Sarauniyar Ingila, Elizabeth ta biyu a shekarar 1953, a madadin majalisar wakilai ta Nijeriya, an kuma bashi nambar girmamawa saboda samun damar halartar shi Bikin.

A shekarar 1954 ne Alhaji Isa Kaita ya tafi aikin Hajjin farko inda ya samu damar ziyartar Makka da Madina. A shekarar da ta biyoni bayanta ta 1955, aka nada shi Amirul Hajji, wato shugaba kuma jagoran Alhazan Nijeriya a kasar Saudiyya. A shekarar 1956, ce sai kuma Sarkin Katsina Usman Nagogo, ya nada shi a mukamin Sarauta ta Madawakin Katsina.

ADVERTISEMENT

A shekarar ce kuma Sarauniyar Elizabeth ta Ingila ta ba shi lambar girmamawa ta O. B. E, duk dai a cikin shekarar ce, aka nada shi Ministan Albarkatun kasa, in da ya canji Mista. Peter Achimugu.

A shekarar 1957 ce aka nada Alhaji Isa Kaita Ministan ilimi in da ya canji Alhaji Aliyu Makaman Bida, mukamin da ya ci gaba da rikewa har zuwa ranar 15 ga watan Janairu 1966. A shekarar 1959 ce, ya kai ziyara zuwa Majalisar Dinkin Duniya da ke birnin New York, domin taimakawa wakilan Ingila a muhawarar, da suka yi lokacin da muka yi nasarar jawo hankalin duniya kan kamaru ta Arewa ta zama wani bangare na Nijeriya har ma aka rika kiran wurin da sunan Sardauna Probince masana tarihi ba za su manta da wannan ba, kai akwai ma wani mawakin Hausa da ya yi wakar North Eastern State da akwai wurin daya ambaci sunan na Sardauna Probince wato lardin da aka mai da shi Lardin Sardauna daga baya, ya kuma ambaci cewar, Maiduguri ce Hedikwatar Jihar Arewa maso gabas ko kuma North Eastern State, yanzu shiyyar ce take da Jihohi shida. Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato ya kai ziyara zuwa kasar Amurka.A shekarar 1962 ce, aka ba shi Lambar girmamawa ta C. B. E., wadda ta fi ta O. B. E., daraja, bugu da kari a wannan shekarar ce aka nada shi mukamin Sarautar gargajiya ta Wazirin Katsina.

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

A shekarar 1963 ce, Alhaji Isa Kaita ya halarci taron majalisar kungiyar kasashen da Ingila ta mulka da aka yi a kasar Malaysia, ya ci gaba da zama wakilin majalisar har tsawon shekaru 14. A shekarar 1964 ce, Gwamnatin Tarayya ta ba shi lambar Yabo ta C. O. N. Inda kuma a ranar 22 ga watan Nuwamba 1965 ne, shugaban jami’ar Ahmadu Bello ta Zariya na wancan lokacin wato Marigayi Sardaunan Sakkwato ya ba shi kyautar Digirin girmamawa na jami’ar, mai suna (Doctor, Of Laws) a Bikin saukar karatun Jami’ar na farko , daga baya kuma a shekarar 1986 ce jami’ar Bayero ta Kano ta sake bashi Digirin girmamawa irin wancan.

Ana gama shi Bikin Saukar karatun ne Alhaji Isa Kaita, ya tashi a jirgin sama daga Kaduna zuwa Legas daga can kuma ya zarce New Zealand, domin halartar taron majalisar wakilai ta kungiyar kasashen da Ingila ta mulka ko rena wanda aka yi a Washington. Alhaji Shehu Shagari, shi ma yana daga cikin wadanda suka halarci taron, ya yi kuma jawabi mai ban sha’awa game da kasar Rhodesia wadda yanzu ake kira da suna Zimbabwe.

Isa kaita
Idris Aliyu Daudawa
+ posts Bio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir
Isa kaita
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

MASU ALAKA

Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Tarihi

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

May 30, 2026
Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya
Tarihi

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

February 22, 2026
Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959
Tarihi

Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959. (2)

January 11, 2026
Next Post
Achraf Hakimi: Sabon Angon Afrika A Harkar Ƙwallon Ƙafa

Achraf Hakimi: Sabon Angon Afrika A Harkar Ƙwallon Ƙafa

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.