ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Alhaji Isa Kaita Wazirin Katsina (2)

by Idris Aliyu Daudawa and Sulaiman
7 months ago
Isa kaita

… ci gaba daga makon da ya gabata.

Bugu da kari ma ya halarci bikin nadin Sarauniyar Ingila, Elizabeth ta biyu a shekarar 1953, a madadin majalisar wakilai ta Nijeriya, an kuma bashi nambar girmamawa saboda samun damar halartar shi Bikin.

A shekarar 1954 ne Alhaji Isa Kaita ya tafi aikin Hajjin farko inda ya samu damar ziyartar Makka da Madina. A shekarar da ta biyoni bayanta ta 1955, aka nada shi Amirul Hajji, wato shugaba kuma jagoran Alhazan Nijeriya a kasar Saudiyya. A shekarar 1956, ce sai kuma Sarkin Katsina Usman Nagogo, ya nada shi a mukamin Sarauta ta Madawakin Katsina.

ADVERTISEMENT

A shekarar ce kuma Sarauniyar Elizabeth ta Ingila ta ba shi lambar girmamawa ta O. B. E, duk dai a cikin shekarar ce, aka nada shi Ministan Albarkatun kasa, in da ya canji Mista. Peter Achimugu.

A shekarar 1957 ce aka nada Alhaji Isa Kaita Ministan ilimi in da ya canji Alhaji Aliyu Makaman Bida, mukamin da ya ci gaba da rikewa har zuwa ranar 15 ga watan Janairu 1966. A shekarar 1959 ce, ya kai ziyara zuwa Majalisar Dinkin Duniya da ke birnin New York, domin taimakawa wakilan Ingila a muhawarar, da suka yi lokacin da muka yi nasarar jawo hankalin duniya kan kamaru ta Arewa ta zama wani bangare na Nijeriya har ma aka rika kiran wurin da sunan Sardauna Probince masana tarihi ba za su manta da wannan ba, kai akwai ma wani mawakin Hausa da ya yi wakar North Eastern State da akwai wurin daya ambaci sunan na Sardauna Probince wato lardin da aka mai da shi Lardin Sardauna daga baya, ya kuma ambaci cewar, Maiduguri ce Hedikwatar Jihar Arewa maso gabas ko kuma North Eastern State, yanzu shiyyar ce take da Jihohi shida. Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato ya kai ziyara zuwa kasar Amurka.A shekarar 1962 ce, aka ba shi Lambar girmamawa ta C. B. E., wadda ta fi ta O. B. E., daraja, bugu da kari a wannan shekarar ce aka nada shi mukamin Sarautar gargajiya ta Wazirin Katsina.

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

A shekarar 1963 ce, Alhaji Isa Kaita ya halarci taron majalisar kungiyar kasashen da Ingila ta mulka da aka yi a kasar Malaysia, ya ci gaba da zama wakilin majalisar har tsawon shekaru 14. A shekarar 1964 ce, Gwamnatin Tarayya ta ba shi lambar Yabo ta C. O. N. Inda kuma a ranar 22 ga watan Nuwamba 1965 ne, shugaban jami’ar Ahmadu Bello ta Zariya na wancan lokacin wato Marigayi Sardaunan Sakkwato ya ba shi kyautar Digirin girmamawa na jami’ar, mai suna (Doctor, Of Laws) a Bikin saukar karatun Jami’ar na farko , daga baya kuma a shekarar 1986 ce jami’ar Bayero ta Kano ta sake bashi Digirin girmamawa irin wancan.

Ana gama shi Bikin Saukar karatun ne Alhaji Isa Kaita, ya tashi a jirgin sama daga Kaduna zuwa Legas daga can kuma ya zarce New Zealand, domin halartar taron majalisar wakilai ta kungiyar kasashen da Ingila ta mulka ko rena wanda aka yi a Washington. Alhaji Shehu Shagari, shi ma yana daga cikin wadanda suka halarci taron, ya yi kuma jawabi mai ban sha’awa game da kasar Rhodesia wadda yanzu ake kira da suna Zimbabwe.

Isa kaita
Idris Aliyu Daudawa
+ posts Bio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund
Isa kaita
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Tarihi

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

May 30, 2026
Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya
Tarihi

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

February 22, 2026
Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959
Tarihi

Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959. (2)

January 11, 2026
Next Post
Achraf Hakimi: Sabon Angon Afrika A Harkar Ƙwallon Ƙafa

Achraf Hakimi: Sabon Angon Afrika A Harkar Ƙwallon Ƙafa

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.