ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Alhaji Isa Kaita Wazirin Katsina (2)

by Idris Aliyu Daudawa and Sulaiman
8 months ago
Isa kaita

… ci gaba daga makon da ya gabata.

Bugu da kari ma ya halarci bikin nadin Sarauniyar Ingila, Elizabeth ta biyu a shekarar 1953, a madadin majalisar wakilai ta Nijeriya, an kuma bashi nambar girmamawa saboda samun damar halartar shi Bikin.

A shekarar 1954 ne Alhaji Isa Kaita ya tafi aikin Hajjin farko inda ya samu damar ziyartar Makka da Madina. A shekarar da ta biyoni bayanta ta 1955, aka nada shi Amirul Hajji, wato shugaba kuma jagoran Alhazan Nijeriya a kasar Saudiyya. A shekarar 1956, ce sai kuma Sarkin Katsina Usman Nagogo, ya nada shi a mukamin Sarauta ta Madawakin Katsina.

ADVERTISEMENT

A shekarar ce kuma Sarauniyar Elizabeth ta Ingila ta ba shi lambar girmamawa ta O. B. E, duk dai a cikin shekarar ce, aka nada shi Ministan Albarkatun kasa, in da ya canji Mista. Peter Achimugu.

A shekarar 1957 ce aka nada Alhaji Isa Kaita Ministan ilimi in da ya canji Alhaji Aliyu Makaman Bida, mukamin da ya ci gaba da rikewa har zuwa ranar 15 ga watan Janairu 1966. A shekarar 1959 ce, ya kai ziyara zuwa Majalisar Dinkin Duniya da ke birnin New York, domin taimakawa wakilan Ingila a muhawarar, da suka yi lokacin da muka yi nasarar jawo hankalin duniya kan kamaru ta Arewa ta zama wani bangare na Nijeriya har ma aka rika kiran wurin da sunan Sardauna Probince masana tarihi ba za su manta da wannan ba, kai akwai ma wani mawakin Hausa da ya yi wakar North Eastern State da akwai wurin daya ambaci sunan na Sardauna Probince wato lardin da aka mai da shi Lardin Sardauna daga baya, ya kuma ambaci cewar, Maiduguri ce Hedikwatar Jihar Arewa maso gabas ko kuma North Eastern State, yanzu shiyyar ce take da Jihohi shida. Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato ya kai ziyara zuwa kasar Amurka.A shekarar 1962 ce, aka ba shi Lambar girmamawa ta C. B. E., wadda ta fi ta O. B. E., daraja, bugu da kari a wannan shekarar ce aka nada shi mukamin Sarautar gargajiya ta Wazirin Katsina.

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

A shekarar 1963 ce, Alhaji Isa Kaita ya halarci taron majalisar kungiyar kasashen da Ingila ta mulka da aka yi a kasar Malaysia, ya ci gaba da zama wakilin majalisar har tsawon shekaru 14. A shekarar 1964 ce, Gwamnatin Tarayya ta ba shi lambar Yabo ta C. O. N. Inda kuma a ranar 22 ga watan Nuwamba 1965 ne, shugaban jami’ar Ahmadu Bello ta Zariya na wancan lokacin wato Marigayi Sardaunan Sakkwato ya ba shi kyautar Digirin girmamawa na jami’ar, mai suna (Doctor, Of Laws) a Bikin saukar karatun Jami’ar na farko , daga baya kuma a shekarar 1986 ce jami’ar Bayero ta Kano ta sake bashi Digirin girmamawa irin wancan.

Ana gama shi Bikin Saukar karatun ne Alhaji Isa Kaita, ya tashi a jirgin sama daga Kaduna zuwa Legas daga can kuma ya zarce New Zealand, domin halartar taron majalisar wakilai ta kungiyar kasashen da Ingila ta mulka ko rena wanda aka yi a Washington. Alhaji Shehu Shagari, shi ma yana daga cikin wadanda suka halarci taron, ya yi kuma jawabi mai ban sha’awa game da kasar Rhodesia wadda yanzu ake kira da suna Zimbabwe.

Isa kaita
Idris Aliyu Daudawa
+ posts Bio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu
Isa kaita
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe
  • Sulaiman
    GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara
  • Sulaiman
    Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026
  • Sulaiman
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

MASU ALAKA

Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Tarihi

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

May 30, 2026
Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya
Tarihi

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

February 22, 2026
Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959
Tarihi

Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959. (2)

January 11, 2026
Next Post
Achraf Hakimi: Sabon Angon Afrika A Harkar Ƙwallon Ƙafa

Achraf Hakimi: Sabon Angon Afrika A Harkar Ƙwallon Ƙafa

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.