ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Alhaji Isa Kaita Wazirin Katsina (2)

by Idris Aliyu Daudawa and Sulaiman
10 months ago
Isa kaita

… ci gaba daga makon da ya gabata.

Bugu da kari ma ya halarci bikin nadin Sarauniyar Ingila, Elizabeth ta biyu a shekarar 1953, a madadin majalisar wakilai ta Nijeriya, an kuma bashi nambar girmamawa saboda samun damar halartar shi Bikin.

A shekarar 1954 ne Alhaji Isa Kaita ya tafi aikin Hajjin farko inda ya samu damar ziyartar Makka da Madina. A shekarar da ta biyoni bayanta ta 1955, aka nada shi Amirul Hajji, wato shugaba kuma jagoran Alhazan Nijeriya a kasar Saudiyya. A shekarar 1956, ce sai kuma Sarkin Katsina Usman Nagogo, ya nada shi a mukamin Sarauta ta Madawakin Katsina.

ADVERTISEMENT

A shekarar ce kuma Sarauniyar Elizabeth ta Ingila ta ba shi lambar girmamawa ta O. B. E, duk dai a cikin shekarar ce, aka nada shi Ministan Albarkatun kasa, in da ya canji Mista. Peter Achimugu.

A shekarar 1957 ce aka nada Alhaji Isa Kaita Ministan ilimi in da ya canji Alhaji Aliyu Makaman Bida, mukamin da ya ci gaba da rikewa har zuwa ranar 15 ga watan Janairu 1966. A shekarar 1959 ce, ya kai ziyara zuwa Majalisar Dinkin Duniya da ke birnin New York, domin taimakawa wakilan Ingila a muhawarar, da suka yi lokacin da muka yi nasarar jawo hankalin duniya kan kamaru ta Arewa ta zama wani bangare na Nijeriya har ma aka rika kiran wurin da sunan Sardauna Probince masana tarihi ba za su manta da wannan ba, kai akwai ma wani mawakin Hausa da ya yi wakar North Eastern State da akwai wurin daya ambaci sunan na Sardauna Probince wato lardin da aka mai da shi Lardin Sardauna daga baya, ya kuma ambaci cewar, Maiduguri ce Hedikwatar Jihar Arewa maso gabas ko kuma North Eastern State, yanzu shiyyar ce take da Jihohi shida. Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato ya kai ziyara zuwa kasar Amurka.A shekarar 1962 ce, aka ba shi Lambar girmamawa ta C. B. E., wadda ta fi ta O. B. E., daraja, bugu da kari a wannan shekarar ce aka nada shi mukamin Sarautar gargajiya ta Wazirin Katsina.

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

A shekarar 1963 ce, Alhaji Isa Kaita ya halarci taron majalisar kungiyar kasashen da Ingila ta mulka da aka yi a kasar Malaysia, ya ci gaba da zama wakilin majalisar har tsawon shekaru 14. A shekarar 1964 ce, Gwamnatin Tarayya ta ba shi lambar Yabo ta C. O. N. Inda kuma a ranar 22 ga watan Nuwamba 1965 ne, shugaban jami’ar Ahmadu Bello ta Zariya na wancan lokacin wato Marigayi Sardaunan Sakkwato ya ba shi kyautar Digirin girmamawa na jami’ar, mai suna (Doctor, Of Laws) a Bikin saukar karatun Jami’ar na farko , daga baya kuma a shekarar 1986 ce jami’ar Bayero ta Kano ta sake bashi Digirin girmamawa irin wancan.

Ana gama shi Bikin Saukar karatun ne Alhaji Isa Kaita, ya tashi a jirgin sama daga Kaduna zuwa Legas daga can kuma ya zarce New Zealand, domin halartar taron majalisar wakilai ta kungiyar kasashen da Ingila ta mulka ko rena wanda aka yi a Washington. Alhaji Shehu Shagari, shi ma yana daga cikin wadanda suka halarci taron, ya yi kuma jawabi mai ban sha’awa game da kasar Rhodesia wadda yanzu ake kira da suna Zimbabwe.

Isa kaita
Idris Aliyu Daudawa
+ posts Bio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Rayuwar Galadiman Kano Alhaji Tijjani Hashim (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kyamar Baƙi: An Sake Kwaso Ƴan Nijeriya 83 Daga Afirka Ta Kudu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 60 Da Kayan Aiki A Edo
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tsohon Shugaban Ƙasa Jonathan Ya Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Ƙasa 18 A Jihar Bauchi
Isa kaita
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Tarihi

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

May 30, 2026
Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya
Tarihi

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

February 22, 2026
Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959
Tarihi

Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959. (2)

January 11, 2026
Next Post
Achraf Hakimi: Sabon Angon Afrika A Harkar Ƙwallon Ƙafa

Achraf Hakimi: Sabon Angon Afrika A Harkar Ƙwallon Ƙafa

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.