• English
  • Business News
Saturday, May 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Masarautar Zazzau Da Sarakunanta (9)

by Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
in Tarihi
0
Tarihin Masarautar Zazzau Da Sarakunanta (9)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)

Tarihin Shugabannin Ƙasar Mali Na Farko A Daular Songhai (7)

Kamar yadda Mudathir Ishak ya yi tsokaci an kafa birnin Zazzau ne a shekarar 1536, miladiyya,a wani yanki na dausayi, kudu da hamada, maraya ce da ta hada manoma da kuma malamai da masu kasuwanci.Sarkin Farko a wancan lokaci sunansa Gunguma dan Bawo.

Bawo kuwa a Hausance shine Bayajidda na Sarauniyar Daurama. Zariya ita ce kanwa ga Sarauniya Amina shine kuma sunan da ta baiwa babban birnin Zazzau,kusa da dutsen Kufaina,a cikin karni na 16 ne aka sanya wa Zazzau wannan suna.

  • Sojoji Sun Aike Da Ƴan Ta’adda 8 Lahira, Sun DaÆ™ile YunÆ™urin Sace Wasu Mutane 28
  • Takaitaccen Nazari A Kan Bishiyar Kanya

Sarauniya Zariya ta gaji Amina wadda rasu a  shekarar 1610 miladiyya a garin Attagara, bayan da ta ci Kano da Katsina da yaki.

Ita ma ta rasu a Yawuri ne, bayan da tayi gajeren mulki. Fadin iyakar inda ta ci da yaki ya kai daga jihar Filato ta yanzu a gabas, zuwa Abuja da kewaye, kamar su Nupe da Nasarawa.

A Arewa kuma har Daura da Katsina ta hadiyo.Ta kuma ta shafe shekaru 30 tana mulki. Mahaifiyarsu ita ce Bakuwa Turunku,ta 22 a jerin sarakunan Zazzau, kafin zuwan fulani. Ita ta kafa garin Turunku, kudu da Zazzau ko Zariya,a kan hanyarta ta zuwa yake-yake da kabilun Nupawa da Gwarawa.Jerin sunayen sarakunan gargajiya da aka yi a Zazzau. Kafin dai fulani su ci Zariya da yaki,a shekarar 1807,an yi sarakuna 60 Hausawa ‘yan asalin garin da yankin, watau sarakunan Habe, wadanda wasunsu sun bi addinan gargajiya, yayin da wasu suka yi addinin musulunci. Sarki Jatau dai a tarihi, wanda yayi mulki ne daga shekarar 1742 zuwa 1802 shi ya fara musulunta ya kuma gina masallaci na farko. Bayan rasuwarsa,sai dansa Makau, ya koma addinin gargajiya, ya kuma rushe masallacin.

Sai dai kuma a shekarar 1804 ce, da Usmanu dan Fodiyo ya fara yin jihadi, Malam Musa,  wanda malami ne kuma bafillace,ya je Gobir inda ya karbo tuta daga Shehu,daganan ya hada karfi da Yamusa, wanda shi ma bafillatanin Borno ne, suka kawo wa Makau yaki. Haka ya sa Makau ya tsere zuwa garin Zuba, inda kusa da inda Babban Birnin Tarayya Abuja take a yanzu, a can ne ya rayu da kabilun yankin har dai ya kai ga rasuwa a can.Malam Musa sai suka tabbatar da abin da mahaifinsa ya faro,watau Masallaci da addinin Islama.

Malam Musa shi ne Sarkin Fulani na Farko, amma ya rasu a a shekarar 1821,daga nan sai Yamusa ya amshi mulki, inda yayi mulki har  ya zuwa shekarar 1834.Daga nan sai Malam Abdulkarim, wanda shi bakatsinene kuma bafillace, ga shi dalibi ga Malam Musa ya karbi mulki.Kuma daga wadannan gidaje ne har yau, ake samar da sarakunan Zariya.1. Mallam Musa (gidan Mallawa) 1804-1821 2. Yamusa (gidan Barnawa) 1821-1834 3. Abdulkarim (gidan Katsinawa) 1834-1846 .4 Hamadu dan Yamusa 1846 5. Muhamman Sani dan Yamusa 1846-1860 6. Sidi Abdulkadir dan Malam Musa 1860 (ture shi aka yi)7.Abdussalami (sullubawa) 1860-1863 8. Abdullahi dan Hamadu dan Yamusa 1863-1873 (an ture shi) sai a 1876-1881 (aka sake ture shi) 9. Abubakar dan Malam Musa 1873-1876 l0. Sambo dan Abdulkarim ( gidan Katsinawa)1881-1890 (shima tumbuke shi aka yi) 11. Yero dan Abdullahi dan Hamadu 1890-1897 12. Kwasau dan Yero 1897-1902 (tumbuke shi aka yi) Zuwan Turawa 13. Aliyu Dan sidi Abdulkadir 1902-1923(shima an tumbuke shi) 14.Dallatu dan Yero 1923-1924 15. IIbrahim dan Kwasau 1924-1936 16. Malam Ja’afar dan Ishak 1936-1959 17. Alamin dan Usman 1959-1975 18.Shehu Idris 1975 zuwa shekarar 2020, daga shi kuma sai Ahmad Nuhu Bamalli wanda aka nada sarauta ranar 8 ga Oktoba 2020 zuwa yanzu.Turawa sun iso da rundunoni na yaki har biyu, a 1900 domin mulkin mallaka.

Jerin sarakunan Suleja da ake kiran su da Sarkin Zazzau Suleja wadanda asalinsu daga can suke.

  1. Muhammadu Makau 1807-1825.
  2. Abubakar Ja (Abuja) 1825-1851.
  3. Abubakar Kwaka Dogon Sarki 1851-1877.
  4. Ibrahim Iyalai Dogon Gwari 1877-1902.
  5. Muhammadu Gani 1902-1917 Ya bar gadon mulki.
  6. Musa Angulu 1917-1944

An samo wannan  Tarihin ne daga encyclopedia ta Hausa


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Masarautar ZazzauTarihi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kosan Dankali Da Nama

Next Post

Tsakanin Maza Da Mata, Wa Ya Fi Kazanta?

Related

Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)
Tarihi

Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)

2 months ago
Tarihin Shugaban Ƙasar Mali Na Farko Sundiata Keita (2)
Tarihi

Tarihin Shugabannin Ƙasar Mali Na Farko A Daular Songhai (7)

2 months ago
A-Ula: Dadadden Birni Mai Cike Da Dinbin Tarihi Da Al’adu
Tarihi

A-Ula: Dadadden Birni Mai Cike Da Dinbin Tarihi Da Al’adu

7 months ago
gusau
Tarihi

Tarihin Gusau Da Sarakunanta (1)

11 months ago
A Tsame Masarautunmu Daga Siyasa
Al'adu

A Tsame Masarautunmu Daga Siyasa

12 months ago
Zazzau
Tarihi

Masarautar Argungu Da Al’adunta (1)

12 months ago
Next Post
Tsakanin Maza Da Mata, Wa Ya Fi Kazanta?

Tsakanin Maza Da Mata, Wa Ya Fi Kazanta?

LABARAI MASU NASABA

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

May 31, 2025
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

May 31, 2025
Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu

Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu

May 30, 2025
Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu

Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu

May 30, 2025
Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta

Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta

May 30, 2025
Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar

Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar

May 30, 2025
Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

May 30, 2025
Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

May 30, 2025
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin

May 30, 2025
Sulhun PDP Ya HaÉ—u Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

Sulhun PDP Ya HaÉ—u Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

May 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.