• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Zanga-zanga A Nijeriya

by Sani Anwar
1 year ago
Zanga-zanga

Gwagwarmayar zanga-zanga a Nijeriya, ta samo asali ce tun lo-kacin mulkin mallaka; inda dandazon mutane suka yi dafifi kan manyan hanyoyi, don nuna rashin amincewarsu da wasu kudire-kudire da kuma salon mulkin Turawan Mulkin Mallaka.

Gwamnatin Turawan Mulkin Mallaka, ta yi matukar mamaki da ganin yadda mata daga gundumar Bendel; wato Abiya kenan suka fito a shekarar 1929, wanda daga bisani aka kira ta da zanga-zangar mata ta Aba, don nuna rashin amincewa da rash-in sanya mata cikin harkokin gudanar da gwamnati; ta hanyar sammacin shugabanni.

  • Shugaban Timor-Leste Ya Yaba Kayayyaki Kirar Kasar Sin
  • Nijeriya Na Kashe Dala Miliyan 600 Wajen Shigo Da Mai Duk Wata – Minista 

Kazalika, akwai kuma zanga-zangar matan Abekuta, wanda kungiyar matan Abekuta ta shirya a shekarar 1940; don nuna rashin amincewa da harajin da Turawan Mulkin Mallakan suka kakaba na rashin adalci.

Haka nan, sai da wannan zanga-zanga ta zama ruwan dare a Nijeriya; har zuwa lokacin samun ‘yancin kai, inda kungiyoyi da dama suka rika yin kiraye-kiraye da babbar murya, don cimma biyan bukatunsu.

A shekarar 1964, an samu mummunar hatsaniya a yankunan Tibi, sakamakon kakaba musu biyan haraji da aka yi na babu gaira babu dalili; wanda zanga-zangar ta yi sanadiyyar rasa dimbin rayuka da dukiyoyi.

LABARAI MASU NASABA

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya

Har ila yau, a lokacin mulkin sojoji; kungiyoyin kwadago da na dalibai da sauran kungiyoyin al’umma, su ne kan gaba wajen jagorantar kowace irin zanga-zanga.

A tarihin zanga-zangar, akwai lokacin da daliban makaranta su-ka jingine karatunsu tare da shiga zanga-zanga; daidai lokacin mulkin tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo; sakamakon cire tallafin karatunsu.

Kazalika, akwai lokacin da daliban suka sake jagorantar wata babbar zanga-zanga a 1989, lokacin da Janar Ibrahim Ba-bangida ya bullo da shirin nan na SAP (Structural Adjustment Programme).

Bugu da kari, masu rajin kare hakkin al’umma da masu son tabbatar da mulkin dimokradiyya, sun tara mutane da dama; don neman ‘yancinsu na dawo da mulkin farar hula, yayin da gwamnatin mulkin soja ta Babangida; ta yi kamar ta yi watsi da alkawarin da ta yi na mika wa gwamnatin dimokradiyya.

Haka wannan zanga-zanga ta yi ta faman afkuwa a lokuta daban-daban na shugabannin Nijeriya, tun daga lokacin mulkin mallaka, sojoji har kawo yanzu da muka samu kanmu a mulkin dimokradiyya ko na farar hula.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja
Manyan Labarai

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

October 17, 2025
Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya
Labarai

Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya

October 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilin Karyewar Farashin Kayan Abinci
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilin Karyewar Farashin Kayan Abinci

October 17, 2025
Next Post
An Kashe Wani Mutum Wajen Zanga-zanga A Jihar Neja

Martanin ‘Yan Adawa Kan Zanga-zanga Da Jawabin Shugaban Kasa

LABARAI MASU NASABA

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

October 17, 2025
peter

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya

Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya

October 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilin Karyewar Farashin Kayan Abinci

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilin Karyewar Farashin Kayan Abinci

October 17, 2025
Tinubu

Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu

October 17, 2025
Shettima

‘Yan Nijeriya Na Dab Da Fita Daga Halin Kuncin Talauci – Shettima 

October 17, 2025
Manzon Allah

Manzon Allah (SAW) Ne Ya Kafa Tushen Wayewar Kai A Duniya

October 17, 2025
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai

Yadda ‘Yan Bindiga Ke Zafafa Hare-hare A Jihohin Arewa Maso Yamma

October 17, 2025
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka: Ta Bar Baya Da Ƙura

October 17, 2025
Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.