• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Zanga-zanga A Nijeriya

by Sani Anwar
1 year ago
Zanga-zanga

Gwagwarmayar zanga-zanga a Nijeriya, ta samo asali ce tun lo-kacin mulkin mallaka; inda dandazon mutane suka yi dafifi kan manyan hanyoyi, don nuna rashin amincewarsu da wasu kudire-kudire da kuma salon mulkin Turawan Mulkin Mallaka.

Gwamnatin Turawan Mulkin Mallaka, ta yi matukar mamaki da ganin yadda mata daga gundumar Bendel; wato Abiya kenan suka fito a shekarar 1929, wanda daga bisani aka kira ta da zanga-zangar mata ta Aba, don nuna rashin amincewa da rash-in sanya mata cikin harkokin gudanar da gwamnati; ta hanyar sammacin shugabanni.

  • Shugaban Timor-Leste Ya Yaba Kayayyaki Kirar Kasar Sin
  • Nijeriya Na Kashe Dala Miliyan 600 Wajen Shigo Da Mai Duk Wata – Minista 

Kazalika, akwai kuma zanga-zangar matan Abekuta, wanda kungiyar matan Abekuta ta shirya a shekarar 1940; don nuna rashin amincewa da harajin da Turawan Mulkin Mallakan suka kakaba na rashin adalci.

Haka nan, sai da wannan zanga-zanga ta zama ruwan dare a Nijeriya; har zuwa lokacin samun ‘yancin kai, inda kungiyoyi da dama suka rika yin kiraye-kiraye da babbar murya, don cimma biyan bukatunsu.

A shekarar 1964, an samu mummunar hatsaniya a yankunan Tibi, sakamakon kakaba musu biyan haraji da aka yi na babu gaira babu dalili; wanda zanga-zangar ta yi sanadiyyar rasa dimbin rayuka da dukiyoyi.

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

Har ila yau, a lokacin mulkin sojoji; kungiyoyin kwadago da na dalibai da sauran kungiyoyin al’umma, su ne kan gaba wajen jagorantar kowace irin zanga-zanga.

A tarihin zanga-zangar, akwai lokacin da daliban makaranta su-ka jingine karatunsu tare da shiga zanga-zanga; daidai lokacin mulkin tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo; sakamakon cire tallafin karatunsu.

Kazalika, akwai lokacin da daliban suka sake jagorantar wata babbar zanga-zanga a 1989, lokacin da Janar Ibrahim Ba-bangida ya bullo da shirin nan na SAP (Structural Adjustment Programme).

Bugu da kari, masu rajin kare hakkin al’umma da masu son tabbatar da mulkin dimokradiyya, sun tara mutane da dama; don neman ‘yancinsu na dawo da mulkin farar hula, yayin da gwamnatin mulkin soja ta Babangida; ta yi kamar ta yi watsi da alkawarin da ta yi na mika wa gwamnatin dimokradiyya.

Haka wannan zanga-zanga ta yi ta faman afkuwa a lokuta daban-daban na shugabannin Nijeriya, tun daga lokacin mulkin mallaka, sojoji har kawo yanzu da muka samu kanmu a mulkin dimokradiyya ko na farar hula.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
Manyan Labarai

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP
Labarai

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
Next Post
An Kashe Wani Mutum Wajen Zanga-zanga A Jihar Neja

Martanin ‘Yan Adawa Kan Zanga-zanga Da Jawabin Shugaban Kasa

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.