• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Zanga-zanga A Nijeriya

by Sani Anwar
10 months ago
in Labarai
0
Masu Zanga-zanga Sun Fito Duk Da Dokar Hana Fita A Jigawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwagwarmayar zanga-zanga a Nijeriya, ta samo asali ce tun lo-kacin mulkin mallaka; inda dandazon mutane suka yi dafifi kan manyan hanyoyi, don nuna rashin amincewarsu da wasu kudire-kudire da kuma salon mulkin Turawan Mulkin Mallaka.

Gwamnatin Turawan Mulkin Mallaka, ta yi matukar mamaki da ganin yadda mata daga gundumar Bendel; wato Abiya kenan suka fito a shekarar 1929, wanda daga bisani aka kira ta da zanga-zangar mata ta Aba, don nuna rashin amincewa da rash-in sanya mata cikin harkokin gudanar da gwamnati; ta hanyar sammacin shugabanni.

  • Shugaban Timor-Leste Ya Yaba Kayayyaki Kirar Kasar Sin
  • Nijeriya Na Kashe Dala Miliyan 600 Wajen Shigo Da Mai Duk Wata – Minista 

Kazalika, akwai kuma zanga-zangar matan Abekuta, wanda kungiyar matan Abekuta ta shirya a shekarar 1940; don nuna rashin amincewa da harajin da Turawan Mulkin Mallakan suka kakaba na rashin adalci.

Haka nan, sai da wannan zanga-zanga ta zama ruwan dare a Nijeriya; har zuwa lokacin samun ‘yancin kai, inda kungiyoyi da dama suka rika yin kiraye-kiraye da babbar murya, don cimma biyan bukatunsu.

A shekarar 1964, an samu mummunar hatsaniya a yankunan Tibi, sakamakon kakaba musu biyan haraji da aka yi na babu gaira babu dalili; wanda zanga-zangar ta yi sanadiyyar rasa dimbin rayuka da dukiyoyi.

Labarai Masu Nasaba

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Har ila yau, a lokacin mulkin sojoji; kungiyoyin kwadago da na dalibai da sauran kungiyoyin al’umma, su ne kan gaba wajen jagorantar kowace irin zanga-zanga.

A tarihin zanga-zangar, akwai lokacin da daliban makaranta su-ka jingine karatunsu tare da shiga zanga-zanga; daidai lokacin mulkin tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo; sakamakon cire tallafin karatunsu.

Kazalika, akwai lokacin da daliban suka sake jagorantar wata babbar zanga-zanga a 1989, lokacin da Janar Ibrahim Ba-bangida ya bullo da shirin nan na SAP (Structural Adjustment Programme).

Bugu da kari, masu rajin kare hakkin al’umma da masu son tabbatar da mulkin dimokradiyya, sun tara mutane da dama; don neman ‘yancinsu na dawo da mulkin farar hula, yayin da gwamnatin mulkin soja ta Babangida; ta yi kamar ta yi watsi da alkawarin da ta yi na mika wa gwamnatin dimokradiyya.

Haka wannan zanga-zanga ta yi ta faman afkuwa a lokuta daban-daban na shugabannin Nijeriya, tun daga lokacin mulkin mallaka, sojoji har kawo yanzu da muka samu kanmu a mulkin dimokradiyya ko na farar hula.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GwagwarmayaNijeriyaTarihiZanga-zanga
ShareTweetSendShare
Previous Post

GORON JUMA’A

Next Post

Martanin ‘Yan Adawa Kan Zanga-zanga Da Jawabin Shugaban Kasa

Related

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

3 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

3 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

13 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

15 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

16 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

16 hours ago
Next Post
An Kashe Wani Mutum Wajen Zanga-zanga A Jihar Neja

Martanin ‘Yan Adawa Kan Zanga-zanga Da Jawabin Shugaban Kasa

LABARAI MASU NASABA

Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.