ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Martanin ‘Yan Adawa Kan Zanga-zanga Da Jawabin Shugaban Kasa

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Zanga-zanga

‘Yan adawa sun mayar da martini kan zanga-zangar da aka gudanarwa a fadin kasar nan, sannan sun kuma mayar da mar-tini kan jawabin da shugaban kasa, Bola Tinubu ya yi kan zanga-zangar. 

Wasu jiga-jigan ‘yan adawa da suka hada da Dakta Umar Ardo, Hajiya Naja’atu Mohammed, Dakta Salihu Lukman da kuma Farfesa Usman Yusuf, sun goyi bayan wadanda suka shirya zanga-zangar a fadin kasar nan; kan halin kunci a Nijeriya.

  • Za Mu Raba Wa Talakawa Kyautar Kudi – Gwamnatin Tarayya
  • Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Ware Biliyan 19 Don Sanya Wa Lawal Kayan Girki

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwar hadin gwiwa da su-ka sanya wa hannu, inda suka bayyana fatansu na ganin cewa; zanga-zangar za ta haifar da sauye-sauyen siyasa da tsari a Arewa da kuma Nijeriya baki-daya.

ADVERTISEMENT

Kazalika, sun tabbatar da cewa; ‘yancin da tsarin mulki ya ba wa dukkan ‘yan kasa damar gudanar da zanga-zanga, sannan kuma sun yarda cewa; dalilin zanga-zangar adawa da tsarin na da inganci kuma ya dace, don haka suka tsaya tsayin daka wajen ganin sun yi amfani da ‘yancinsu na yin zanga-zangar.

Tsohon mataimakin shugaban kasa, kuma dan takarar shuga-ban kasa a karkashin inuwar jam’iyyar PDP a zaben 2023, ya yi Allah wadai da amfani da harsashi kan ‘yan kasa da ke zanga-zangar lumana, kan matsin rayuwa da tabarbarewar tattalin ar-ziki.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Atiku ya yi wannan kakkausan lafazi ne, yayin da ake ci gaba da gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa a Nijeriya, inda wasu jihohi aka samu hargitsi tsakanin jami’an tsaro da masu zanga-zangar kamar Kano da Abuja da kuma Kaduna.

Zanga-zangar da aka fara gudanarwa daga 1 zuwa 10 ga watan Agusta, an samu rahotannin asarar rayuka, lalatawa tare da wawure dukiyar gwamnati da al’ummar kasa a wasu jihohin kasar nan.

Atiku ya bayyana matakin jami’an tsaro na yin amfani da harsashi kan masu zanga-zangar da cewa, “abu ne mai muni da ya yi kama da zamanin mulkin kama-karya na soji.”

Haka nan ita ma babbar jam’iyyar adawa ta PDP ta ce, Shugaba Bola Tinubu; sam bai damu da halin da ‘yan kasar ke ciki ba, duk da zanga-zangar da ake gudanarwa.

A cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Lahadi, wadda ta samu sa hannun sakataren yada labarunta na kasa, Debo Ologunagba, PDP ta ce; jawabin Tinubu ya nuna yadda karara APC da Shugaba Tinubu ba su damu da halin kuncin da al’ummar kasar ke ciki ba.

Zanga-zangar, wadda ta fara a ranar Alhamis ta rikide zuwa ri-kici a wasu jihohin, lamarin da ya kai ga asarar rayuka da duki-yar al’umma.

Tinubu dai ya bukaci masu zanga-zangar da su janye tare da bude kofar yin zama, domin tattaunawa.

Yanzu haka dai, al’amura na kara ta’azzara a wasu jihohi kamar Filato, Kaduna da kuma Bauchi, inda jihohin suka sanya dokar hana fita a ranar Litinin.

A Jihohin Kano, Yobe da Katsina kuwa; gwamnatocin jihohin sun sassauta dokar hana fitar ne duk da cewa, ana ci gaba da gudanar da zanga-zangar.

PDP ta ce, abin da Tinubu da jami’yyarsa ke nuna wa ‘yan Nijer-iya; alama ce ta cewa kasar ba a gabansu take ba.

Haka kuma, ‘yan adawan sun caccaki Shugaban Kasa Tinubu; kan jawabin da ya gabatar wa ‘yan kasa kai tsaye a safiyar La-hadi.

Jam’iyyar PRP a nata bangaren kuma, ta bukaci Shugaban Kasa Tinubu ya saurari bukatun masu zanga-zangar ta hanyar rage kudin gudanar da gwamnatinsa tare da kawar da cin hanci da rashawa da kuma almubazzaranci.

Shugaban jam’iyyar PRP na kasa, Dakta Falalu Bello; shi ya bay-yana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a Abuja, inda ya cewa; hakki ne da ‘yan kasa suke da shi na yin zanga-zanga da kuma gudanar da ‘yancinsu.

Sai dai, ya bukaci masu zanga-zangar su gudanar da ita cikin lumana ba tare da tashin hankali ba.

Haka zalika, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a zaben 2023, Peter Obi; ya koka da gazawar gwamnatin tarayya wajen magance bukatun da suka rura wutar zanga-zangar yunwa a fadin kasar baki-daya.

Obi ya bayyana hakan ne, a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Tuwita a ranar Litinin, inda ya bukaci shugaban kasar ya ni-santa kansa daga wasu mutanen da suka kewaye shi marasa gaskiya da kishin kasa.

Obi ya kuma bukaci gwamnati, da ta yi kokarin gano masu ai-kata laifukan da ke yunkurin kawo cikas ga zanga-zangar ta hanyar satar dukiyar jama’a da sauran munanan dabi’u da ku-ma kare wadanda ke aiwatar da hakkinsu na dimokuradiyya.

Shi ma Atiku, ya caccaki jawabin shugaban kasar, inda ya ce; jawabin na cike ne da rudani, sannan ya kasa warware matsalolin da ‘yan Nijeriya ke ciki.

Atiku, wanda ya yi magana ta bakin mai ba shi shawara kan harkokin yada labarai, Paul Ibe, a wata sanarwa da ya fitar a Abuja ya ce, jawabin shugaban kasar babu abin da ya yi illa kara tunzara masu zanga-zangar.

Zanga-zanga
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Rana Ta 3: Duk Da Dokar Hana Fita Masu Zanga-zanga Sun Fito A Kano

Tattalin Arzikin Nijeriya Na Fuskantar Koma Baya Sakamakon Zanga-zanga

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.