Shugaba Bola Tinubu da sauran shugabannin ƙasashen Yammacin Afrika sun gudanar da wani taron gaggawa ta Intanet a ranar Alhamis domin tattauna juyin mulki a Guinea-Bissau.
Sojoji sun kifar da gwamnati a ranar Laraba tare da tsare Shugaba Umaro Sissoco Embaló, sannan suka naɗa Janar Horta Nta Na Man a matsayin shugaban riƙon ƙwarya na shekara guda.
- Sin Ta Kasance Mai Goyon Bayan Kasashen Afirka Wajen Zamanantar Da Kansu
- Gwamnan Bauchi Ya Gabatar Da Naira Biliyan 878 A Matsayin Kasafin 2026
Tinubu ya halarci taron ECOWAS daga Abuja, inda shugabannin suka tattauna kan halin da ake ciki da matakan da ya dace ƙungiyar ta ɗauka, kasancewar ECOWAS na adawa da juyin mulkin soja.
Taron ya nuna damuwar ƙungiyar kan yawaitar juyin mulki a yankin, da kuma ƙoƙarinta na kare dimokuraɗiyya da tabbatar da zaman lafiya a ƙasashen Yammacin Afrika.
Tsohon shugaban Nijeriya, Goodluck Jonathan yana Guinea-Bissau lokacin da sojoji suka kifar da gwamnatin ƙasar.














