ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekara 25 Da Kafa ACF: Nasarori, Matsaloli Da Ƙalubale

by Shehu Yahaya and Sulaiman
6 months ago
Acf

A yayin da matsalolin tsaro ke kara kamari a Arewacin Nijeriya, kungiyar Tuntuba ta Arewa (Arewa Consultatibe Forum) ta gudanar da taron bikin cikar ta shekaru 25 da kafuwa, inda ta tattauna kan matsalolin tsaro, ci gaban yankin da kuma hanyoyin da za a bi domin inganta zaman lafiya.

Duk da zaman zullumi da tashin kwanciyar hankali sakamakon sace zaliban makarantu a jihohin Kebbi da Neja bai hana kungiyar dattawan Arewa  gudanar da taron ba  inda taron  ya mayar da hankali kan batun tsaro da makomar yankin Arewa.

  • G20: Kaduna Ce Jihar Da Tafi Dacewa Da Zuba Jari A Nijeriya – Gwamna Uba Sani 
  • Gwamnan Bauchi Ya Gabatar Da Naira Biliyan 878 A Matsayin Kasafin 2026

A yayin taron wanda ya gudana a Jihar Kaduna, kungiyar ta ACF ta bayyana takaici da damuwarta dangane da yadda matsalar tsaro ke kara kamari a yankin Arewa.

ADVERTISEMENT

Tun farko da yake jawabi Shugaban Majalisar Amintattu na kungiyar Alhaji Bashir M. Dalhatu, Wazirin Dutse, ya koka dangane da yadda yankin arewa ya zamo tamkar filin yaki, inda ake kisa da yin garkuwa da mutane a kullum, inda yace lallai wannan abin takaici ne da ya zama dole a dauki mataki akai.

Ya kuma jaddada aniyar kungiyar na samar da hazin kai da bin ka’idojin gudanarwa tsakanin mambobin kungiyar domin bayar da gudunmawar da ta kamata wajen ciyar da yankin gaba.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Alhaji Dalhatu ya jaddada bukatar daidaito da taka-tsantsan wajen isar da sako ga jama’a musamman ga jami’an kungiyar da ke hulda da kafafen watsa labarai gabanin babban zaben 2027.

Ya gargadi masu kafa kungiyoyi daban-daban a Arewa, yana kiran irin wadannan kungiyoyi “barazana ga hazin kan Arewa.” Haka kuma ya yaba wa sojojin Nijeriya bisa kokarinsu da sadaukarwa wajen yaki da matsalar tsaro.

Alhaji Dalhatu ya kuma yi Allah wadai da “aungiyoyin marasa kishin kasa” da suka jawo rikicin baya-bayan nan a matatar mai ta Dangote, tare da kira ga Gwamnatin Tarayya da ta shiga tsakani.

A cewarsa, kwanan nan an samu rikice-rikicen maganganu masu karo da juna daga wasu jami’an ACF a matakin kasa da jihohi, wanda hakan ya sa dole a kafa tsarin sadarwa mai tsauri.

A jawaban da suka gabatar a wajen taron manyan Attajiran nan biyu daga jihar Kano Alhaji Aliko Dangote d Abdulsamad Isiyaka Rabi’u, sun bayyana yadda matsalar tsaro ke shafar harkar kasuwanci a Arewa, inda suka bukaci ‘yan arewa da su bayar da dukkanin gudummawar da ta kamata wajen shawo kan matsalar.

A jawabin Shugaban kasa Tinubu wanda ya samu wakilcin shugaban majalisar dokokin tarayya Abbas Tajuddeen ya bayyana damuwarsa kan yadda harkar tsaro ke kara tabarbarewa a yankin Arewa, inda ya bayyana aniyar gwamnati na daukar matakan gaggawa domin shawo kan matsalar.

A zantawarsa da wakilinmu jim kadan bayan kammala taron, Shugaban Rundunar Talakawan Nijeriya Malam Imrana Nas, ya bayyana cewa akwai bukatar Dattawan arewa su dage wajen Samar sa gwamnati irin halin sa yankin Arewa take ciki musamman a bangare matsalar tsaro sa talauci da rashin aikinyi.

Ya baya da kokarin kungiyar ya ACF wajen tattaro manyan ‘Yan Arewa domin tattauna matsalolin da suka shafi ci gaban yankin.

Imrana Nas ya bayyana craw gwamnati ba ta nuna cikakkiyar shirye-shiryen kawo karshen matsalolin tsaro a Arewacin Nijeriya ba, duk da karuwar hare-haren ’yan bindiga da ta’addanci a yankin.

Imrana Nas ya ce hare-haren da ake ta fama da su a ya kin sun nuna cewa tsarin yaki da ’yan ta’adda bai kai matsayin da ake bukata ba. Ya ce idan ana son a magance matsalar gaba daya, sai an zarce matakan da ake dauka yanzu.

Ya nuna rashin gamsuwarsa akan matakan da ake dauka wajen yin sasanci da ‘yan ta’adda Inda yace akwai lauje cikin nadi .

“ Wadanan mutane da ake kira da ‘Yan ta’adda basu fi karfin gwamnati ba kuma baza su fi karfin gwamnati ba sai dai akwai lauje cikin nadi wannan halin ya sa aka barsu suke yin abinda suke so amma fa ba don gwamnati bazata iya maganinsu ba. Nayi imani da Allah da kasar Yarabawa ne ko Inyamurai da baza su amince ba da tuni ankai karshen wannan fitinar. Mu yanzu idan gwamnati ba zata iya ba to zamu hadu ci gaba da kumumuwar addu’a kamar yadda mukayi kamin zuwan Buhari shugaban kasa “

“ Yanzu Fa dan ta’adda ne zaizo ayi sasanci da shi da bindigar shi zaizo a gama sasanci kuma ya dauki bindigarshi ya koma da ita, wai mutumin da kake nema ruwa a jallo sai gashi yazo inda kake kuma kun gama magana ya koma kaga ba’a shirya maganin wadannan mutanan ba; ba’a shirya fada dasu ba”

Imrana Nas ya kara da cewa matsalar tana da tushe mai zurfi, ciki har da talauci, da taoron Mutuwa, su kuma shugabanni sun komai san duniya duk da irin makudan kudazen da ake warewa a harkar. Ya ce dole gwamnati ta karkata hankali wajen addu’a tunda alamu sun nuna gwamnati kamar bazata iya ba.”

A yanzu haka, al’ummar Arewa na ci gaba da fatan gwamnati ta kara daukar matakai masu karfi domin dakile ayyukan ta’addanci, yayin da suka bayyana damuwa kan yadda matsalar ke kara ta’azzara a wasu yankuna.

Taron dai ya samu halartar manyan jama’a daga dukkanin fadin arewacin Nijeriya harda makwabta inda a karshen taron a karrama wasu manyan ‘yan arewa wadanda suka hada da tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, da Namadi Sambo da Dangote da Isiyaka Rabi’u da sauran jama’a da dama, inda aka tara kudi sama da Naira Biliyan 90

Masana tsaro da suka yi jawabi a taron sun yi bayanin cewa karuwar hare-haren ’yan bindiga da rawar da wasu tsageru ke takawa wajen sace-sacen dalibai abu ne mai nassaba da karancin kayan aiki, rashin wadatattun jami’an tsaro da kuma rashin tsarin kula da iyakokin Arewa.

Acf
Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Bayan Shehu Sani Ya Ƙalubalanci Zailani, Rikicin APC Ya Ƙara Zafi A Kaduna
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ya Dace ‘Yan Arewa Su Ƙara Marawa Tinubu Baya Domin Kammala Wa’adi Na Biyu — Shehu Sani
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Zargin Ware Ɓangaren El-rufa’i: Rikicin Cikin Gida Ya Kaure A Jam’iyyar ADC, Kaduna
Acf
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Mutane 7 Ne Suka Rasu Sakamakon Zazzabin Cizon Sauro Da Taifod Ba Wata Sabuwar Cuta Ba – Gwamnatin Kano

Buƙatar Daƙile Kutsen ‘Yan Bindiga Na Iyakokin Jihar Kano

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.