• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Ci Amanar Kano, Babu Batun Haɗin Guiwa Tsakaninsa Da Kwankwaso A 2027 – Galadima

by Sadiq
4 days ago
in Manyan Labarai, Siyasa
0
Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jigo a jam’iyyar NNPP, Buba Galadima, ya ce babu batun yin haɗin gwiwa tsakanin Shugaba Bola Tinubu da tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, kafin zaɓen 2027.

Yayin hira da gidan talabijin na Channels, Galadima ya zargi gwamnatin Tinubu da cin amanar Kwankwaso da NNPP a Kano, ta hanyar mara wa tsohon Sarkin Kano, Aminu Ado Bayero, baya duk da cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf ya tsige shi ta hanyar doka.

  • Manoma Na Neman Ɗauki Bayan Ambaliya Ta Lalata Gonakin Shinkafa A Kebbi
  • Dole Ne A Nace Kan Manufar Sin Daya Tak Don Kiyaye Zaman Lafiya A Mashigin Taiwan

“Ta yaya Kwankwaso zai yi abota da APC alhali suna yi mana haka a Kano? Sun kafa sarakuna biyu a gari guda; na Gwamnatin Tarayya da na Gwamnatin jiha. Wa ke da ikon naɗa Sarki da biyan albashinsa?” in ji Galadima.

Ya ƙara da cewa Gwamnatin Tarayya na kare Aminy Ado Bayero ta hanyar samar masa da jami’an tsaro yayin da matsalar tsaro ke ƙara ta’azzara a wasu yankuna na Kano.

“Sun bai wa Sarkinsu (Aminu Ado Bayero) motocin ‘yansanda kusan 40 cike da jami’an Mopol, amma a wasu wurare a Kano ana kashe mutane, ana ƙwace musu wayoyi, amma ‘yansanda sun maƙale a waje ɗaya. Wannan ai abin kunya ne,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

Galadima, ya tabbatar da cewa NNPP za ta taka muhimmiyar rawa wajen fitar da shugaban Nijeriya a 2027.

“Mu ne za mu yanke wanda zai zama shugaban ƙasa a 2027,” in ji shi, yana mai ƙaryata batun cewa Kwankwaso zai yi sulhu da Tinubu.

Ya ƙara da cewa: “Kar wani ya fito ya ce Kwankwaso zai shiga APC. Idan an nemi yin hakan zan sani. Kwankwaso ɗaya ne daga cikin manyan ‘yan siyasa a Nujeriya yanzu, ya ƙalubalanci APC a Kano ya kuma kayar da su.”

Rigimar sarautar Kano ta ƙara dagula siyasar jihar.

A shekarar 2014, Muhammadu Sanusi II ya zama Sarkin Kano bayan rasuwar marigayi Ado Bayero.

Amma a 2020, tsohon Gwamnan jihar Abdullahi Ganduje ya tsige shi, ya naɗa Aminu Ado Bayero.

A watan Mayun 2024, Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya dawo da Sanusi II, lamarin da ya jawo Aminu Ado Bayero ya tafi kotu.

Tun daga wannan lokaci aka jibge jami’an tsaron tarayya a fadar da Aminu Ado Bayero ke zaune duk da cewa an tsige shi.

Galadima, ya ce Gwamnatin Tarayya na goyon bayan Bayero ne kawai saboda siyasa.

“Suna tunanin zai taimaka musu a 2027, amma babu wani Sarkin Kano da ya taɓa tantance wanda zai zama shugaban ƙasa,” in ji shi.

Jihar Kano ce ke da mafi yawan masu kaɗa ƙuri’a a Nijeriya.

A zaɓen 2023, ta kaɗa kusan ƙuri’u miliyan 1.7.

Kwankwaso ya fi kowa samu ƙuri’u, inda ya samu 997,279, Tinubu ya samu 517,341, Atiku Abubakar ya tashi da 131,716, yayin da Peter Obi ya samu 28,513.

Duk da cewa Kwankwaso ya zo na huɗu a zaɓen shugaban ƙasa da ƙuri’u miliyan 1.49, NNPP ta lashe zaɓe a ƙananan hukumomi 38 daga 44 a Kano, lamarin da ya nuna tasirinta a Arewa.

A halin yanzu, Gwamna Abba Kabir Yusuf na NNPP ne ke mulkin jihar, amma APC na riƙe da kujeru biyu daga cikin uku na Sanata a Kano, abin da ke nuna cewa za a kai ruwa rana a zaɓen 2027.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Aminu Ado BayeroBuba GaladimaCin AmanakanoKwankwasoSanusi IISarakunaSiyasaTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Manoma Na Neman Ɗauki Bayan Ambaliya Ta Lalata Gonakin Shinkafa A Kebbi

Next Post

Akpabio Ya Ƙaryata Jita-jitar Ba Shi Da Lafiya

Related

Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

12 hours ago
Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 
Siyasa

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

15 hours ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

19 hours ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

22 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

23 hours ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

1 day ago
Next Post
Akpabio Ya Ƙaryata Jita-jitar Ba Shi Da Lafiya

Akpabio Ya Ƙaryata Jita-jitar Ba Shi Da Lafiya

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.