• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Isa Guinea-Bissau Domin Taron ECOWAS, Ya Ziyarci Sojojin Nijeriya

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Tinubu Ya Isa Guinea-Bissau Domin Taron ECOWAS, Ya Ziyarci Sojojin Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan nasarar da ya samu a wajen taron ‘Sabuwar Yarjejeniyar Kudade ta Duniya’ da aka yi a birnin Paris na kasar Faransa, wanda Shugaba Emmanuel Macron ya karbi bakunci, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya isa Bissau, babban birnin Jamhuriyar Guinea-Bissau, domin halartar taro na 63 na shugabannin kasashen kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka (ECOWAS).

Shugaba Tinubu ya kuma yi amfani da damar taron wajen ziyartar rundunar sojojin Nijeriya da ke kasar a karkashin kungiyar ECOWAS.

  • Gwamnatin Gombe Ta Sha Alwashin Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya
  • Sharhi: Sin Da Amurka Ba Su Bukatar Zama Abokan Gabar Juna 

A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar, Dele Alake ya fitar, ya ce taron na 63 da zai gudana a ranar Lahadi 9 ga watan Yulin 2023, zai kasance karo na farko da shugaban kasar zai gudanar da harkokin kasa da kasa a nahiyar Afirka tun bayan hawansa mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2023.

Shugaba Tinubu, wanda jirginsa ya sauka a filin tashi da saukar jiragen sama na kasa da kasa da ke birnin Bissau da misalin karfe 5:30 na yammacin ranar Asabar, ya kasance abun jan hankali.

Ana sa ran shugabannin yankin 16 za su yi jawabi kan wasu muhimman batutuwan da suka shafi yankin da suka hada da rahoton zaman taro na 50 na kwamitin sulhu na MDD wanda ya kunshi kalubalen tsaro da kasashe mambobin kungiyar ke fuskanta.

Labarai Masu Nasaba

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Sauran batutuwan da shugabannin za su tattauna sun hada da rahoton halin da ake ciki a Jamhuriyar Mali, Burkina Faso da Guinea.

Bayan isowarsa, shugaba Tinubu ya ziyarci dakarun Nijeriya karkashin kungiyar ECOWAS da ke kasar Guinea-Bissau.

Ya bayyana godiyarsa ga sojojin da kwamandansu Janar Al-hassan Grema bisa sadaukarwa da hidimar da suke yi wa Nijeriya da kuma kasar da ta karbi bakuncinsu, ya kuma kara da cewa Nijeriya za ta ci gaba da tallafawa dimokuradiyya a yammacin Afirka da ma duniya baki daya.

“Na zo nan ne domin nuna goyon baya a gare ku, ina so in tabbatar muku cewa mun kuduri aniyar tallafawa zaman lafiya da dimokuradiyya ba kawai a yammacin Afirka ba har ma a duniya baki daya.

“Nijeriya kasa ce da ta yi kaurin suna a Saliyo da Laberiya da sauran wurare, muna fatan za ku goyi bayan kare tsarin mulkin kasa.

“Muna alfahari da ku, muna alfahari da amincinku, Nijeriya ta dogara da ku, za a samu zaman lafiya da ci gaba a kasarmu,” in ji shugaban.

Birgediya Janar Grema ya bayyana jin dadin sojojin ga shugaba Tinubu saboda kasancewarsa babban kwamanda na farko a tarihin Nijeriya da ya ziyarci sojojinsa a wajen gabar tekun kasar.

A yayin da yake ziyara a kasar Guinea-Bissau, shugaban na Nijeriya zai gudanar da tarukan kasashen biyu tare da yin wasu ayyuka a gefen taron.

A cikin tawagar shugaban kasar a wannan tafiya akwai mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, mukaddashin gwamnan babban bankin kasa, Dokta Folashodun Shonubi; Babban Sakataren Ma’aikatar Harkokin Waje, Ambasada Adamu Ibrahim Lamuwa; Babban Sakataren Ma’aikatar Tsaro, Dokta Ibrahim Kana; Babban Sakatare na Ma’aikatar Kudi, Aliyu Ahmed da Wakilin ECOWAS, Ambasada Musa Nuhu.

Sauran da ke cikin tawagar sun hada da tsoffin gwamnoni, Sanata Abubakar Atiku Bagudu (Kebbi), Abdullahi Ganduje (Kano), Abubakar Badaru (Jigawa) da kuma Sanata Abu Ibrahim daga jihar Katsina.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ECOWASTaroTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Gombe Ta Sha Alwashin Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya

Next Post

Abin Da Ya Sa A Daminar Da Ta Gabata Masara Ta Yi Tsada -Shugaba

Related

JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

60 minutes ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

6 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

10 hours ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

11 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

1 day ago
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

1 day ago
Next Post
Abin Da Ya Sa A Daminar Da Ta Gabata Masara Ta Yi Tsada -Shugaba

Abin Da Ya Sa A Daminar Da Ta Gabata Masara Ta Yi Tsada -Shugaba

LABARAI MASU NASABA

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.