• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Isa Guinea-Bissau Domin Taron ECOWAS, Ya Ziyarci Sojojin Nijeriya

by Sadiq
2 years ago
Tinubu

Bayan nasarar da ya samu a wajen taron ‘Sabuwar Yarjejeniyar Kudade ta Duniya’ da aka yi a birnin Paris na kasar Faransa, wanda Shugaba Emmanuel Macron ya karbi bakunci, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya isa Bissau, babban birnin Jamhuriyar Guinea-Bissau, domin halartar taro na 63 na shugabannin kasashen kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka (ECOWAS).

Shugaba Tinubu ya kuma yi amfani da damar taron wajen ziyartar rundunar sojojin Nijeriya da ke kasar a karkashin kungiyar ECOWAS.

  • Gwamnatin Gombe Ta Sha Alwashin Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya
  • Sharhi: Sin Da Amurka Ba Su Bukatar Zama Abokan Gabar Juna 

A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar, Dele Alake ya fitar, ya ce taron na 63 da zai gudana a ranar Lahadi 9 ga watan Yulin 2023, zai kasance karo na farko da shugaban kasar zai gudanar da harkokin kasa da kasa a nahiyar Afirka tun bayan hawansa mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2023.

Shugaba Tinubu, wanda jirginsa ya sauka a filin tashi da saukar jiragen sama na kasa da kasa da ke birnin Bissau da misalin karfe 5:30 na yammacin ranar Asabar, ya kasance abun jan hankali.

Ana sa ran shugabannin yankin 16 za su yi jawabi kan wasu muhimman batutuwan da suka shafi yankin da suka hada da rahoton zaman taro na 50 na kwamitin sulhu na MDD wanda ya kunshi kalubalen tsaro da kasashe mambobin kungiyar ke fuskanta.

LABARAI MASU NASABA

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

Sauran batutuwan da shugabannin za su tattauna sun hada da rahoton halin da ake ciki a Jamhuriyar Mali, Burkina Faso da Guinea.

Bayan isowarsa, shugaba Tinubu ya ziyarci dakarun Nijeriya karkashin kungiyar ECOWAS da ke kasar Guinea-Bissau.

Ya bayyana godiyarsa ga sojojin da kwamandansu Janar Al-hassan Grema bisa sadaukarwa da hidimar da suke yi wa Nijeriya da kuma kasar da ta karbi bakuncinsu, ya kuma kara da cewa Nijeriya za ta ci gaba da tallafawa dimokuradiyya a yammacin Afirka da ma duniya baki daya.

“Na zo nan ne domin nuna goyon baya a gare ku, ina so in tabbatar muku cewa mun kuduri aniyar tallafawa zaman lafiya da dimokuradiyya ba kawai a yammacin Afirka ba har ma a duniya baki daya.

“Nijeriya kasa ce da ta yi kaurin suna a Saliyo da Laberiya da sauran wurare, muna fatan za ku goyi bayan kare tsarin mulkin kasa.

“Muna alfahari da ku, muna alfahari da amincinku, Nijeriya ta dogara da ku, za a samu zaman lafiya da ci gaba a kasarmu,” in ji shugaban.

Birgediya Janar Grema ya bayyana jin dadin sojojin ga shugaba Tinubu saboda kasancewarsa babban kwamanda na farko a tarihin Nijeriya da ya ziyarci sojojinsa a wajen gabar tekun kasar.

A yayin da yake ziyara a kasar Guinea-Bissau, shugaban na Nijeriya zai gudanar da tarukan kasashen biyu tare da yin wasu ayyuka a gefen taron.

A cikin tawagar shugaban kasar a wannan tafiya akwai mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, mukaddashin gwamnan babban bankin kasa, Dokta Folashodun Shonubi; Babban Sakataren Ma’aikatar Harkokin Waje, Ambasada Adamu Ibrahim Lamuwa; Babban Sakataren Ma’aikatar Tsaro, Dokta Ibrahim Kana; Babban Sakatare na Ma’aikatar Kudi, Aliyu Ahmed da Wakilin ECOWAS, Ambasada Musa Nuhu.

Sauran da ke cikin tawagar sun hada da tsoffin gwamnoni, Sanata Abubakar Atiku Bagudu (Kebbi), Abdullahi Ganduje (Kano), Abubakar Badaru (Jigawa) da kuma Sanata Abu Ibrahim daga jihar Katsina.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah
Manyan Labarai

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

November 7, 2025
Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump
Manyan Labarai

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

November 7, 2025
Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 
Manyan Labarai

Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 

November 7, 2025
Next Post
Abin Da Ya Sa A Daminar Da Ta Gabata Masara Ta Yi Tsada -Shugaba

Abin Da Ya Sa A Daminar Da Ta Gabata Masara Ta Yi Tsada -Shugaba

LABARAI MASU NASABA

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

November 7, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

November 7, 2025
Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

November 7, 2025
Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

November 7, 2025
Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

November 7, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

November 7, 2025
An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

November 7, 2025
Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.