• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Isa Guinea-Bissau Domin Taron ECOWAS, Ya Ziyarci Sojojin Nijeriya

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Tinubu Ya Isa Guinea-Bissau Domin Taron ECOWAS, Ya Ziyarci Sojojin Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan nasarar da ya samu a wajen taron ‘Sabuwar Yarjejeniyar Kudade ta Duniya’ da aka yi a birnin Paris na kasar Faransa, wanda Shugaba Emmanuel Macron ya karbi bakunci, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya isa Bissau, babban birnin Jamhuriyar Guinea-Bissau, domin halartar taro na 63 na shugabannin kasashen kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka (ECOWAS).

Shugaba Tinubu ya kuma yi amfani da damar taron wajen ziyartar rundunar sojojin Nijeriya da ke kasar a karkashin kungiyar ECOWAS.

  • Gwamnatin Gombe Ta Sha Alwashin Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya
  • Sharhi: Sin Da Amurka Ba Su Bukatar Zama Abokan Gabar Juna 

A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar, Dele Alake ya fitar, ya ce taron na 63 da zai gudana a ranar Lahadi 9 ga watan Yulin 2023, zai kasance karo na farko da shugaban kasar zai gudanar da harkokin kasa da kasa a nahiyar Afirka tun bayan hawansa mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2023.

Shugaba Tinubu, wanda jirginsa ya sauka a filin tashi da saukar jiragen sama na kasa da kasa da ke birnin Bissau da misalin karfe 5:30 na yammacin ranar Asabar, ya kasance abun jan hankali.

Ana sa ran shugabannin yankin 16 za su yi jawabi kan wasu muhimman batutuwan da suka shafi yankin da suka hada da rahoton zaman taro na 50 na kwamitin sulhu na MDD wanda ya kunshi kalubalen tsaro da kasashe mambobin kungiyar ke fuskanta.

Labarai Masu Nasaba

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

Sauran batutuwan da shugabannin za su tattauna sun hada da rahoton halin da ake ciki a Jamhuriyar Mali, Burkina Faso da Guinea.

Bayan isowarsa, shugaba Tinubu ya ziyarci dakarun Nijeriya karkashin kungiyar ECOWAS da ke kasar Guinea-Bissau.

Ya bayyana godiyarsa ga sojojin da kwamandansu Janar Al-hassan Grema bisa sadaukarwa da hidimar da suke yi wa Nijeriya da kuma kasar da ta karbi bakuncinsu, ya kuma kara da cewa Nijeriya za ta ci gaba da tallafawa dimokuradiyya a yammacin Afirka da ma duniya baki daya.

“Na zo nan ne domin nuna goyon baya a gare ku, ina so in tabbatar muku cewa mun kuduri aniyar tallafawa zaman lafiya da dimokuradiyya ba kawai a yammacin Afirka ba har ma a duniya baki daya.

“Nijeriya kasa ce da ta yi kaurin suna a Saliyo da Laberiya da sauran wurare, muna fatan za ku goyi bayan kare tsarin mulkin kasa.

“Muna alfahari da ku, muna alfahari da amincinku, Nijeriya ta dogara da ku, za a samu zaman lafiya da ci gaba a kasarmu,” in ji shugaban.

Birgediya Janar Grema ya bayyana jin dadin sojojin ga shugaba Tinubu saboda kasancewarsa babban kwamanda na farko a tarihin Nijeriya da ya ziyarci sojojinsa a wajen gabar tekun kasar.

A yayin da yake ziyara a kasar Guinea-Bissau, shugaban na Nijeriya zai gudanar da tarukan kasashen biyu tare da yin wasu ayyuka a gefen taron.

A cikin tawagar shugaban kasar a wannan tafiya akwai mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, mukaddashin gwamnan babban bankin kasa, Dokta Folashodun Shonubi; Babban Sakataren Ma’aikatar Harkokin Waje, Ambasada Adamu Ibrahim Lamuwa; Babban Sakataren Ma’aikatar Tsaro, Dokta Ibrahim Kana; Babban Sakatare na Ma’aikatar Kudi, Aliyu Ahmed da Wakilin ECOWAS, Ambasada Musa Nuhu.

Sauran da ke cikin tawagar sun hada da tsoffin gwamnoni, Sanata Abubakar Atiku Bagudu (Kebbi), Abdullahi Ganduje (Kano), Abubakar Badaru (Jigawa) da kuma Sanata Abu Ibrahim daga jihar Katsina.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ECOWASTaroTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Gombe Ta Sha Alwashin Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya

Next Post

Abin Da Ya Sa A Daminar Da Ta Gabata Masara Ta Yi Tsada -Shugaba

Related

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano
Manyan Labarai

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

13 hours ago
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

18 hours ago
Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata
Manyan Labarai

Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

22 hours ago
Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama
Manyan Labarai

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

24 hours ago
HaÉ—akar Jam’iyyun Adawa Ba Ya ÆŠaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC
Manyan Labarai

HaÉ—akar Jam’iyyun Adawa Ba Ya ÆŠaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

1 day ago
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

1 day ago
Next Post
Abin Da Ya Sa A Daminar Da Ta Gabata Masara Ta Yi Tsada -Shugaba

Abin Da Ya Sa A Daminar Da Ta Gabata Masara Ta Yi Tsada -Shugaba

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sake Kashe Mutum 6 A Ƙauyukan Filato, Sun Jikkata Wasu

Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato

July 2, 2025
An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.