• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Gombe Ta Sha Alwashin Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya

by Yunusa Isa
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Gombe Ta Sha Alwashin Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakataren Gwamnatin Jihar Gombe Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi, ya bayyana cewa nan bada daɗewa ba gwamnatin jihar za ta magance rikicin manoma da makiyaya daya daɗe yana haifar da babbar barazanar tsaro a ƙasar nan.

Njoɗi ya bayyana hakan ne yayin da ya karɓi baƙuncin shugabannin tawagar aiwatar da Shirin Zamanantarwa da Bunƙasa Kiwo wato (L-PRES) yayin wata ziyara da suka kai masa a gidan gwamnati.

  • ‘Muna Cikin Fargabar Yiwuwar Ambaliyar Ruwa A Daminar Bana’
  • Sharhi: Sin Da Amurka Ba Su Bukatar Zama Abokan Gabar Juna 

Ya ce shirin wanda Bankin Duniya ke ɗaukar nauyi, an samar da shi ne sakamakon siyasantar da shirin bunƙasa kiwo na gwamnatin tarayya, wanda aka tsara da nufin zamanantar da sana’ar, saɓanin yadda ake yinta a fili sakaka, lamarin da ke haddasa rikici tsakanin manoma da makiyaya a kasar nan.

Sakataren gwamnatin ya ce duba da ɗimbin damammakin da Jihar Gombe ke da su a harkar noma da kiwo, da kuma babban gandun kiwon da ta ke da shi na Wawa-Zange, gwamnan jihar, Muhammadu Inuwa Yahaya ya ga wajibcin lalubo sabbin hanyoyin cin gajiyar arziƙin da Allah ya huwacewa jihar don amfanin al’ummarta.

Da yake yabawa tawagar bisa jajircewarta na ganin an inganta kiwon a ƙarƙashin sabon shirin da jihar ta shiga, sakataren ya koka da cewa Nijeriya ba ta cin moriyar arziƙin dabbobinta yadda ya kamata.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

“Ba ma morar arziƙin dabbobin da muke da su yadda ya kamata. Babu wani abu da za a ce ya zama shara a yau, ƙasashen da suka ci gaba suna amfani da komai na dabbobi.”

“Akwai wasu hanyoyin da za mu ƙara amfana da waɗannan dabbobi ban da madara da nama; me muke yi da jinin da ke zuba a banza? Ana iya iya amfani da shi wajen yin abincin wassu dabbobin, abin da ƙasashen da suka ci gaba suke yi ke nan. Ƙashin fa me muke yi da shi?, Mai laushin kawai muke ci, mu zubar da mai taurin, za a iya amfani da shi ta wasu hanyoyin. Ina hanji da sauran kayan ciki? Wasu daga ciki kawai ake amfani da su a watsar da sauran, za a iya amfani da su a matsayin taki da sauran fa’idodi” in ji shi.

Ya ce baya ga alfanun shirin ta fuskar tattalin arzikin, L-PRES zai taimaka wajen samar da dauwamammiyar mafita ga matsalar tsaron da ta samo asali daga rikicin manoma da makiyaya a kasar nan.

Da yake yabawa tawagar aiwatar da shirin bisa jajircewarta da ya kai ta ga samun lamunin na Bankin Duniya don gudanar da shirin, Njoɗi ya buƙaci shugabannin shirin su yi watsi da duk wani nau’in alfarma ko sanayya tare da yin waje da duk wanda bai shirya bada gudummawar da za ta kai ga samun nasarar shirin ba.

Njoɗi ya yi gargaɗin cewa “Yanzu za a iya cewa kuna yi wa Bankin Duniya aiki ne, kuma shi bai san wata abota, zumunta ko dangantaka ba, abin da yake so kawai shi ne ku yi aiki a yi nasara. Don haka kar ku bamu kunya. Mun sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna da bankin, yanzu wannan shiri ya zama namu. Idan wani ya ƙi yin abin da ya kamata, ku shaida mana za mu kore shi”.

Ya buƙaci shugabannin shirin na L-PRES kar su yi ƙasa a gwiwa, su jajirce wajen ganin tattalin arzikin Jihar Gombe da na manoma da makiyaya ya bunƙasa.

Ya kuma bada tabbacin gwamnatin jihar na ci gaba da bai wa shirin haɗin kai da goyon baya don samun nasararsa.

Tun farko a jawabinsa, shugaban tawagar kuma kodinetan shirin Dokta Usman Bello Abubakar, ya ce shirin an samar da shi ne da nufin faɗaɗa harkokin noma a jihar, musamman a ɓangaren kiwo.

Ya ƙara da cewa shirin zai kuma magance rikicin manoma da makiyaya da ke ci gaba da salwantar da rayuka da dukiyoyi a jihar dama Nijeriya.

Ya ce kiwo sana’a ce mai riba wadda ke inganta tattalin arzikin ɗaiɗaikun jama’a, da na jiha da ma ƙasa baki ɗaya.

Da yake bayyana cewa Jihar Gombe ce ta uku a Nijeriya wajen cika sharuɗan samun lamunin Bankin Duniya, kodinetan ya yabawa gwamnan jihar, da kuma goyon baya da kyakkywan jagorancin da sakataren gwamnatin jihar ke bai wa tawagar.

Tawagar ta taya Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya murnar sake zaɓensa, da kuma Farfesa Njoɗi bisa sake naɗin da aka yi masa a matsayin sakataren gwamnatin jihar, inda ya bayyana Njoɗi a matsayin shugaba mai sauƙin kai a mu’amala kuma jagora abun koyi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GombegwamnatiMakiyayaManomaRikici
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Muna Cikin Fargabar Yiwuwar Ambaliyar Ruwa A Daminar Bana’

Next Post

Tinubu Ya Isa Guinea-Bissau Domin Taron ECOWAS, Ya Ziyarci Sojojin Nijeriya

Related

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
Da ɗumi-ɗuminsa

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

4 hours ago
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a
Labarai

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

5 hours ago
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson
Labarai

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

6 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

9 hours ago
Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da Ɗaliban Kaduna Kyauta A Bas
Labarai

Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da Ɗaliban Kaduna Kyauta A Bas

12 hours ago
Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos
Labarai

Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos

13 hours ago
Next Post
Tinubu Ya Isa Guinea-Bissau Domin Taron ECOWAS, Ya Ziyarci Sojojin Nijeriya

Tinubu Ya Isa Guinea-Bissau Domin Taron ECOWAS, Ya Ziyarci Sojojin Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

July 6, 2025
Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.