• Leadership Hausa
Sunday, June 4, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaraba Ga Mata: Hanyoyin Mallakar Miji Cikin Sauki

by Rabi'at Sidi Bala
5 months ago
in Rahotonni
0
Tsaraba Ga Mata: Hanyoyin Mallakar Miji Cikin Sauki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

In kina son ki shawo kan wuta ko ki kashe ta gaba daya ba wata wutar za ki kara mata ba, nemo ruwa mai sanyi ki kwara mata ki sa ido ki gani in za ta ci gaba da habaka, haka namiji ya ke. Da wasu shawarwar a kan yadda za mallaki mijin ki.

-Namiji bai son a ce kina ba shi umurni, bare a ce kina yi masa nasiha, duk kuwa da cewa yana bukatar nasihar a zahiri, don haka in kina bukatar zuwa wani wuri kar ki ce masa “Zani wuri kaza” ki saka ta a sigar tambaya “Ina son na tambaye ka ne, dama na so zuwa wuri kaza ne” ko in kina bukatar wani abu kar ki ce “Ka ba ni kaza zan yi kaza” ki zabi lafazin da za ki yi aiki da shi, kamar ki ce “Muna bukatar abu kaza ko za sayo ne?” Da duk irin lafazin da ke nuna girmamawa da bukatar abin a wurinsa, wata gatsar take fadi, har ma ta kara da cewa “In ba haka ba sai dai a zauna haka”.

  • Amfanin Lalle Wajen Gyaran Fata
  • Jami’an Tsaro Sun Kuɓutar Da Wata Soja Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Iyakar Enugu Da Imo

 -In kuma dawowa gida ya yi, tarbe shi ku shigo tare, in yana rike da wani abin, karba masa, sai dai in ya nuna ba ya so, kamar jakar kudi da wasu abubuwa da suke bukatar sirri, kar ki yi irin abin da wasu matan suke yi, wadanda ko matsawa daga inda suke ba sa yi, sai dai su ce “Sannu da zuwa!”.

-In kuwa ya fadi maganar da kike ganin cewa kuskure ce kar ki ce ba haka ba, ki jinjina wa tunaninsa ki bar shi haka, daga baya ki dawo da ita ta wata sigar ki ba shi shawara a kai yadda ba zai fahimci cewa fito na fito kike yi da fahimtarsa ba.

– In kuma ya yi miki ba dai-dai ba kar ki kullace shi, bare har ki ce za ki rama, yafe masa, wata rana zai kyautata miki, namiji ne.

Labarai Masu Nasaba

Shanuna Sun Fi Saukin Kiwo A Kan Mulkin Nijeriya – Buhari

Nijeriya Ce Ta 37 A Kasashen Da Suka Fi Fama Da Ciwon Siga -Kididdiga

– Duk kyautar da ya yi miki ko da ba ki bukatarta, ki nuna masa godiyarki tamkar ba abin da kike so kamarta, daga baya bayan ya manta ki nuna masa wata wace ta fi wannan, don kar ya kara kawo miki ta farko.

– In za ku shiga wuri tare ki dan yi baya shi ya fara yin gaba, sai in shi ne ya ba ki damar ki wuce.

– In yana karanto miki matsalolin da ake ciki, ki  zabi kalmomin da za ki rika karfafa masa gwiwa, ki rika yaba wa irin kokarin da yake yi duk da matsalolin da yake fadi.

– Kar ki yarda gardama ta rika hada ku, ba ta karewa da kyau, in ya ja ki sake, shi da kansa zai gano bai yi dai-dai ba, wasu mazan su kan ba da hakuri, wasu kuma sai dai su yi ta janki da wasa ko su yi miki kyautar da ba su yi niyya ba.

– In kika ba shi shawara bai dauka ba daga baya abin ya cabe masa kar ki ce “Ai dama na gaya maka” ki nuna masa damuwarki.

– In kika roke shi wani abin ya ce ba shi da shi kar ki nuna rashin jin dadinki, yabe shi ki ce “Ai kai mai yi ne, tun da ka ce babu wallahi na san babu ne, amma Allah ba zai barka haka ba zai kawo in sha Allah”.

– In ya kawo miki matsalolin ‘yan uwansa ki nuna damuwarki, kar kare su kar ki zarge su, sai iya gama ki ya ba masa a kan hakurin da yake yi da su, ki karfafa masa gwiwa, ko da kuwa kin san ba wani abin da yake yi na a zo a gani.

– In zai fita ki raka shi har bakin kofa.

– Ki tabbatar ya sa kaya masu kyau, ki goge masa takalmansa.

Tags: Malakar MijiMataMijiTsaraba
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rashin Bai Wa Mata Kulawar Da Ta Dace Daga Maza Masu Harkar Kwallo

Next Post

Yanzu-Yanzu: Tsohon Paparoma Benedict XVI Ya Rasu Yana Da Shekaru 95

Related

Shanuna Sun Fi Saukin Kiwo A Kan Mulkin Nijeriya – Buhari
Rahotonni

Shanuna Sun Fi Saukin Kiwo A Kan Mulkin Nijeriya – Buhari

1 day ago
Nijeriya Ce Ta 37 A Kasashen Da Suka Fi Fama Da Ciwon Siga -Kididdiga
Rahotonni

Nijeriya Ce Ta 37 A Kasashen Da Suka Fi Fama Da Ciwon Siga -Kididdiga

1 day ago
Yadda Mohammed Bello Koko Ya Tsaftace Hukumar Tashoshin Ruwan Nijeriya
Rahotonni

Yadda Mohammed Bello Koko Ya Tsaftace Hukumar Tashoshin Ruwan Nijeriya

2 days ago
Yadda Amurka Ta Yi Kokarin Amfani Da Nukiliya Wajen Tarwatsa Wata
Rahotonni

Yadda Amurka Ta Yi Kokarin Amfani Da Nukiliya Wajen Tarwatsa Wata

5 days ago
Yadda Cutar Hawan Jini Ke Kisan Mummuke A Nijreriya
Rahotonni

Yadda Cutar Hawan Jini Ke Kisan Mummuke A Nijreriya

1 week ago
Wata Kungiyar Siyasa Ta Yi Allah Wadai Da Rusau A Jihar Kaduna
Rahotonni

Ragargazar Sallama Da El-Rufa’i Ke Yi A Kaduna

1 week ago
Next Post
Yanzu-Yanzu: Tsohon Paparoma Benedict XVI Ya Rasu Yana Da Shekaru 95

Yanzu-Yanzu: Tsohon Paparoma Benedict XVI Ya Rasu Yana Da Shekaru 95

LABARAI MASU NASABA

Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 

Gwamna Yusuf Ya Kori Jami’an Cibiyar Alhazan Kananan Hukumomi 44 Na Jihar Kano

June 4, 2023
Me Ya Sa BRICS Ke Kara Samun Karbuwa Daga Kasashen Duniya

Me Ya Sa BRICS Ke Kara Samun Karbuwa Daga Kasashen Duniya

June 4, 2023
Sana’ar Kwalliya

Sana’ar Kwalliya

June 4, 2023
Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli

Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli

June 4, 2023
Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

June 4, 2023
Takaitaccen Tarihin Ka’idojin Rubutun Hausa (II)

Takaitaccen Tarihin Ka’idojin Rubutun Hausa (II)

June 4, 2023
Dalilin Da Manoman Rama A Jihar Katsina Ke Kara Habaka

Dalilin Da Manoman Rama A Jihar Katsina Ke Kara Habaka

June 4, 2023
Farashin Tumatir Ya Karye Bayan Ghana Da Kamaru Sun Turo Shi Kasuwannin Nijeriya

Farashin Tumatir Ya Karye Bayan Ghana Da Kamaru Sun Turo Shi Kasuwannin Nijeriya

June 4, 2023
Shanun Buhari Sun Ragu Saboda Yawan Kyautarsa — Garba Shehu

Shanun Buhari Sun Ragu Saboda Yawan Kyautarsa — Garba Shehu

June 4, 2023
Babu Gaskiya A Labarin Mutuwar Akeredolu -Gwamnatin Ondo

Babu Gaskiya A Labarin Mutuwar Akeredolu -Gwamnatin Ondo

June 3, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.