ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Ƙaddamar Da Jakadun Wayar Da Kai Game Da Rigakafi

by Hussein Yero
1 month ago
Zamfara

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta ƙaddamar da jakadun wayar da kai game da  alluran rigakafin yara da ƙarfafa kiwon lafiya a matakin farko a jihar, a taron da aka gudanar a Cibiyar Kiwon Lafiya ta Farko ta Dr. Karima da ke Tudun Wada, Gusau.

Taron ya samu halartar jami’an gwamnati, da Sarakunan gargajiya, da shugabannin ƙananan hukumomi da ƙungiyoyin bayar da tallafi. Hajiya Huriyya ta bayyana gangamin a matsayin wani muhimmin mataki na kare rayukan yara, tana mai jaddada cewa haɗin gwuiwa tsakanin iyaye, da al’umma da shugabanni na da matuƙar muhimmanci wajen ƙaruwar amsar rigakafi.

  • Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara
  • Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

A wajen taron, Uwargidan Gwamnan ta rantsar da Maman Jakadu, matan shugabannin ƙananan hukumomi – waɗanda za su na isar da bayanai ga al’ummomi don ƙarfafar iyaye su kai ƴaƴansu rigakafi kafin haihuwa da bayan haihuwa. Ta ce jita-jita da labaran ƙarya game da rigakafi na kawo cikas, inda ta tabbatar da cewa duk alluran da ake amfani da su a Nijeriya suna da aminci kuma babu wata illa da ke tattare da su. Ta yabawa sarakuna da malamai bisa rawar da suke takawa wajen ƙarfafa wayar da kan jama’a.

ADVERTISEMENT

Babban Sakataren hukumar lula da lafiya a matakin farko a jihar, Dakta Hussaini Anka, ya bayyana cewa an samu gagarumar nasara cikin watanni 11 da suka gabata ta fuskar raguwar cututtukan da rigakafi ke iya hanawa, sakamakon sabbin shirye-shiryen ceton rai da aka aiwatar. Ya ce Gwamna Dauda Lawal ya kashe sama da Naira biliyan biyu don gyaran cibiyoyin lafiya 147 a matakin farko, a ƙoƙarin magance ƙarancin amsar rigakafi da tabbatar da cewa jama’a na samun kulawa kai tsaye.

Sarkin Zamfaran Anka, Alhaji Attahiru Ahmad, ya buƙaci iyaye su karɓi rigakafi don ƴaƴansu ba tare da tsoro ko shakka ba, yana mai jaddada cewa Majalisar Koli ta Addinin Musulunci ta tabbatar da cewa rigakafi ba shi da wata matsala ga lafiya. Ya ce masarautun gargajiya za su ci gaba da tallafa wa gwamnati wajen yaƙi da cututtukan da za a iya maganinsu, domin tabbatar da cewa duk wani yaro a Zamfara ya samu kariyar da ta dace.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Ake Amfani Da ‘Ya’yan Gwanda A Samu Lafiya

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban
Kiwon Lafiya

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
Yadda Ake Amfani Da ‘Ya’yan Gwanda A Samu Lafiya
Kiwon Lafiya

Yadda Ake Amfani Da ‘Ya’yan Gwanda A Samu Lafiya

December 14, 2025
Zamfara
Kiwon Lafiya

Amfanin Zogale Ga Lafiyar Jikin Ɗan’adam

December 6, 2025
Next Post
Ƙungiyar IPOB Ta Yi Watsi Da Hukuncin Ɗaurin Rai-Da-Rai Ga Nnamdi Kanu

Ƙungiyar IPOB Ta Yi Watsi Da Hukuncin Ɗaurin Rai-Da-Rai Ga Nnamdi Kanu

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.