ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Ƙaddamar Da Jakadun Wayar Da Kai Game Da Rigakafi

by Hussein Yero
6 months ago
Zamfara

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta ƙaddamar da jakadun wayar da kai game da  alluran rigakafin yara da ƙarfafa kiwon lafiya a matakin farko a jihar, a taron da aka gudanar a Cibiyar Kiwon Lafiya ta Farko ta Dr. Karima da ke Tudun Wada, Gusau.

Taron ya samu halartar jami’an gwamnati, da Sarakunan gargajiya, da shugabannin ƙananan hukumomi da ƙungiyoyin bayar da tallafi. Hajiya Huriyya ta bayyana gangamin a matsayin wani muhimmin mataki na kare rayukan yara, tana mai jaddada cewa haɗin gwuiwa tsakanin iyaye, da al’umma da shugabanni na da matuƙar muhimmanci wajen ƙaruwar amsar rigakafi.

  • Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara
  • Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

A wajen taron, Uwargidan Gwamnan ta rantsar da Maman Jakadu, matan shugabannin ƙananan hukumomi – waɗanda za su na isar da bayanai ga al’ummomi don ƙarfafar iyaye su kai ƴaƴansu rigakafi kafin haihuwa da bayan haihuwa. Ta ce jita-jita da labaran ƙarya game da rigakafi na kawo cikas, inda ta tabbatar da cewa duk alluran da ake amfani da su a Nijeriya suna da aminci kuma babu wata illa da ke tattare da su. Ta yabawa sarakuna da malamai bisa rawar da suke takawa wajen ƙarfafa wayar da kan jama’a.

ADVERTISEMENT

Babban Sakataren hukumar lula da lafiya a matakin farko a jihar, Dakta Hussaini Anka, ya bayyana cewa an samu gagarumar nasara cikin watanni 11 da suka gabata ta fuskar raguwar cututtukan da rigakafi ke iya hanawa, sakamakon sabbin shirye-shiryen ceton rai da aka aiwatar. Ya ce Gwamna Dauda Lawal ya kashe sama da Naira biliyan biyu don gyaran cibiyoyin lafiya 147 a matakin farko, a ƙoƙarin magance ƙarancin amsar rigakafi da tabbatar da cewa jama’a na samun kulawa kai tsaye.

Sarkin Zamfaran Anka, Alhaji Attahiru Ahmad, ya buƙaci iyaye su karɓi rigakafi don ƴaƴansu ba tare da tsoro ko shakka ba, yana mai jaddada cewa Majalisar Koli ta Addinin Musulunci ta tabbatar da cewa rigakafi ba shi da wata matsala ga lafiya. Ya ce masarautun gargajiya za su ci gaba da tallafa wa gwamnati wajen yaƙi da cututtukan da za a iya maganinsu, domin tabbatar da cewa duk wani yaro a Zamfara ya samu kariyar da ta dace.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida

Zamfara
Hussein Yero
+ postsBio
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero-2/
    Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero-2/
    Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero-2/
    Ramadan: Hon Jaji Ya Ƙaddamar Da Tallafin Abinci Ga Mutane Sama Da 500,000 A Zamfara
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero-2/
    Dauda Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Almajirai 17 Da Suka Rasu A Sakamakon Tashin Gobara A Zamfara

MASU ALAKA

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir
Kiwon Lafiya

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

May 30, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Kiwon Lafiya

Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida

May 23, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Yi Wa Mutane 6,842 Tiyata Kyauta A Kashi 17 Na Shirin Tallafin Lafiya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Yi Wa Mutane 6,842 Tiyata Kyauta A Kashi 17 Na Shirin Tallafin Lafiya

May 21, 2026
Next Post
Ƙungiyar IPOB Ta Yi Watsi Da Hukuncin Ɗaurin Rai-Da-Rai Ga Nnamdi Kanu

Ƙungiyar IPOB Ta Yi Watsi Da Hukuncin Ɗaurin Rai-Da-Rai Ga Nnamdi Kanu

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.