• English
  • Business News
Sunday, July 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Isra’ila

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 weeks ago
in Daga Birnin Sin
0
Wang Yi Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Isra’ila
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya Asabar 14 ga wata, mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar, Wang Yi, ya tattauna ta wayar tarho da ministan harkokin wajen kasar Iran, Abbas Araqchi.

Wang Yi ya bayyana cewa, a fili kasar Sin tana Allah wadai da matakin kasar Isra’ila, na keta hurumin kasar Iran a fannonin mulkin kai, da tsaro da kuma cikakken ‘yancin yankinta, tana kuma adawa da irin munanan hare-haren da ake kai wa jami’an Iran da fararen hula na kasar, kana kasar Sin tana goyon bayan Iran kan yadda take kokarin kare mulkin kai, da hakki da moriyarta, da tabbatar da tsaron jama’ar kasar.

  • Babban Hafsan Soji Ya Ƙalubalanci Sabbin Sojoji Da Su Shirya Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda
  • NAF Na Shirin Siyo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu Daga Amurka

Wang ya ce, kasar Sin tana son ci gaba da yin mu’amala da Iran da dukkan bangarorin da abin ya shafa, da kuma ci gaba da taka rawa wajen sa kaimi ga sassauta yanayin da ake ciki.

A nasa bangare, Abbas Araqchi ya bayyana godiyarsa ga kasar Sin bisa yadda take fahimtar ra’ayin kasar Iran da nuna mata goyon baya, kuma ya yi imanin cewa, kasar Sin za ta taka muhimmiyar rawa wajen inganta zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

Sa’an nan, duk dai a jiya 14 ga wata, Wang Yi ya tattauna ta wayar tarho da ministan harkokin wajen kasar Isra’ila, Gideon Sa’ar. Bayan sauraron ra’ayin bangaren Isra’ila kan halin da ake ciki da kuma matsayin da kasar ke dauka, Wang Yi ya bayyana cewa, a ko da yaushe kasar Sin tana ba da shawarar cewa, ya kamata a warware duk wata takaddama ta kasa da kasa ta hanyar tattaunawa da shawarwari, kuma tana adawa da amfani da karfin tuwo da takunkumi.

Labarai Masu Nasaba

Sin Da Myanmar Da Thailand Za Su Fatattaki Zambar Da Ake Yi Ta Hanyoyin Sadarwar Waya

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

Bisa la’akari da haka, a fili kasar Sin tana adawa da matakin da Isra’ila ta dauka na keta dokokin kasa da kasa, inda ta kai wa kasar Iran hari, lamarin da ba za a amince da shi ba, musamman ma ta la’akari da yadda kasashe daban daban ke ci gaba da neman hanyar daidaita batun nukiliyar kasar ta Iran ta hanyar siyasa.

Wang Yi ya bayyana cewa, kasar Sin ta bukaci Isra’ila da Iran da su warware sabanin dake tsakaninsu ta hanyar yin shawarwari, da lalubo bakin zaren kasancewa tare cikin kwanciyar hankali da lumana. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

APCn Kaduna Ta Mara Wa Tinubu, Uba Sani Da Kakakin Majalisa Abbas Baya Don Wa’adi Na Biyu

Next Post

Ganduje Ya Noƙe Kan Furta Ko Shettima Zai Yi Takara Da Tinubu A 2027

Related

Sin Da Myanmar Da Thailand Za Su Fatattaki Zambar Da Ake Yi Ta Hanyoyin Sadarwar Waya
Daga Birnin Sin

Sin Da Myanmar Da Thailand Za Su Fatattaki Zambar Da Ake Yi Ta Hanyoyin Sadarwar Waya

31 minutes ago
Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali
Daga Birnin Sin

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

18 hours ago
Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal
Daga Birnin Sin

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

19 hours ago
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

20 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

21 hours ago
Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu
Daga Birnin Sin

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

23 hours ago
Next Post
Ganduje Ya Noƙe Kan Furta Ko Shettima Zai Yi Takara Da Tinubu A 2027

Ganduje Ya Noƙe Kan Furta Ko Shettima Zai Yi Takara Da Tinubu A 2027

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Myanmar Da Thailand Za Su Fatattaki Zambar Da Ake Yi Ta Hanyoyin Sadarwar Waya

Sin Da Myanmar Da Thailand Za Su Fatattaki Zambar Da Ake Yi Ta Hanyoyin Sadarwar Waya

July 6, 2025
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

July 6, 2025
Arsenal Ta Kammala Daukar Martin Zubimendi Daga Real Sociedad

Arsenal Ta Kammala Daukar Martin Zubimendi Daga Real Sociedad

July 6, 2025
Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da Ɗaliban Kaduna Kyauta A Bas

Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da Ɗaliban Kaduna Kyauta A Bas

July 6, 2025
Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos

Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos

July 6, 2025
Kofin Duniya: Real Madrid Za Ta Fara Da PSG A Semi Final

Kofin Duniya: Real Madrid Za Ta Fara Da PSG A Semi Final

July 6, 2025
Chelsea Ta Kammala Ɗaukar Jamie Gittens Daga Borussia Dortmund

Chelsea Ta Kammala Ɗaukar Jamie Gittens Daga Borussia Dortmund

July 6, 2025
Tsoro, Fargaba Da Wahala: ‘Bala’in Da Muka Gani A Yakin Sudan

Tsoro, Fargaba Da Wahala: ‘Bala’in Da Muka Gani A Yakin Sudan

July 6, 2025
Bayern Munich Ta Fara Zawarcin Marcus Rashford

Bayern Munich Ta Fara Zawarcin Marcus Rashford

July 6, 2025
Gobe Za A Fara Wasannin Kofin Afirka Na Mata

Gobe Za A Fara Wasannin Kofin Afirka Na Mata

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.