ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Amurka Ta Daina Sa Hannu Cikin Harkokin Najeriya

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 weeks ago
Amurka

Bisa labarin da jaridar ‘The Punch’ ta Najeriya ta bayar, an ce, a kwanan nan kwamitocin majalisar dokokin Amurka sun gudanar da taro, don tantance lamuran garkuwa da mutane da ke faruwa a Najeriya, da kuma batun zargin da aka yi cewa wai ana cin zarafin Kiristoci a kasar. Kafin hakan, shugaban Amurka Donald Trump ya furta a shafinsa na sada zumunta cewa, Najeriya ta zama “wuri mai barazana ga rayuwar mabiyan addinin Kirista”, ya kuma sake sanya Najeriya a cikin jerin kasashe da ake sa musu kulawar musamman bisa dokar ‘yancin addini ta kasa da kasa, kana ya umurci ma’aikatar tsaro ta Amurka, da ta shirya wajen daukar matakin soji a Najeriya idan hakan ya zama wajaba.

To ko me ya sa Amurka ta sa hannu cikin harkokin gidan Najeriya ba zato ba tsammani? Kuma ko mene ne ainihin burinta?

Lallai, Amurka tana zargin Nijeriya da “cin zarafin Kiristoci a Najeriya”, amma gaskiyar lamarin shi ne, mafi yawan rikice-rikice da ke faruwa a Najeriya suna da alaka da kwaton albarkatu da rikice-rikicen kabilu, yayin da kungiyar masu tsattsauran ra’ayi ta “Boko Haram”, ke kai hare-hare ba tare da bambanta wani addini ba. Ko musulmai ma suna cikin wadanda abin ya fi shafa. Don hakan zargin na “kisan kiyashi na addini” ba shi da tushe balle makama.

ADVERTISEMENT

A bangaren siyasar cikin gidan Amurka, shugaba Trump yana amfani da “kare mabiyan addinin Kirista” don neman gamsar da masu jefa masa kuri’a mabiyan addinin kirista ‘yan bushara, don samun goyon bayansu, tare da dora laifi kan saura game da matsalolin tattalin arziki da rashin aikin yi a cikin Amurka.

A fannin tattalin arziki kuma, Najeriya a matsayinta na kasar da ta fi yawan samar da mai a Afirka, Amurka ta matsawa Najeriya lamba ne da nufin mallakar makamashinta da sauran muhimman albarkatu, tare da raunana tasirin wasu kasashe a fannin hadin gwiwar makamashi tsakaninsu da Najeriya.

LABARAI MASU NASABA

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Ta Yaya Za A Iya Tabbatar Da Tsaro A Yammacin Afirka?

A sa’i daya kuma, Najeriya muhimmiyar kasa ce a yankin yammacin Afirka. Amurka na neman shiga fagen tsaron Najeriya ne ta hanyar fakewa da batun “hadin gwiwar tsaro”, don dakile yunkurin adawa da kasashen yamma a yammacin Afirka, tare da tilasta wa Najeriya nuna goyon bayanta.

Sai kuma ta fannin dangantakar Najeriya da Amurka, game da harajin da Amurka ta kakabawa sassa daban daban, shugaban Najeriyar Bola Tinubu ya taba cewa: “Idan kudaden shigarmu da ba na bangarorin mai ba suna karuwa, ba za mu ji tsoron duk wani abu da Trump ke yi ba.” Kazalika, a babban taron MDD na karo na 80, mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima ya zargin matakan da Isra’ila ta dauka a Gaza, da kuma asarar rayukan Palasdinawa da hakan ya haifar. Hakan ne ma ya sanya kafofin yada labarai na Amurka, suka karawa labaran tashe-tashen hankula na cikin gidan Najeriya gishiri, don mai da martani ga Najeriya kan wadannan batutuwa.

A duniyar yau, yawancin kasashe suna mayar da hankali kan zaman lafiya da ci gaba, suna kara hadin gwiwa don cin moriya tare. Irin wannan dabaru da Amurka ke dauka na yin barazana, da matsin lamba, da sanya takunkumi bisa karfinta sam ba su dace ba. Dole ne ‘yan Najeriya su jagoranci kansu, su magance matsalolin Najeriya da karfin kansu. Kamata ya yi Amurka ta daina sa hannu cikin harkokin cikin gidan Najeriya. (Mai rubutu: MINA)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Ta Yaya Za A Iya Tabbatar Da Tsaro A Yammacin Afirka?
Ra'ayi Riga

Ta Yaya Za A Iya Tabbatar Da Tsaro A Yammacin Afirka?

December 17, 2025
Me Ya Sa Aka Kayyade Yin Amfani Da Sinadaran Narkar Da Kankara A Beijing
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Kayyade Yin Amfani Da Sinadaran Narkar Da Kankara A Beijing

December 16, 2025
Next Post
Xi Jinping Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Faransa 

Xi Jinping Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Faransa 

LABARAI MASU NASABA

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.