ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Amurka Ta Daina Sa Hannu Cikin Harkokin Najeriya

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
Amurka

Bisa labarin da jaridar ‘The Punch’ ta Najeriya ta bayar, an ce, a kwanan nan kwamitocin majalisar dokokin Amurka sun gudanar da taro, don tantance lamuran garkuwa da mutane da ke faruwa a Najeriya, da kuma batun zargin da aka yi cewa wai ana cin zarafin Kiristoci a kasar. Kafin hakan, shugaban Amurka Donald Trump ya furta a shafinsa na sada zumunta cewa, Najeriya ta zama “wuri mai barazana ga rayuwar mabiyan addinin Kirista”, ya kuma sake sanya Najeriya a cikin jerin kasashe da ake sa musu kulawar musamman bisa dokar ‘yancin addini ta kasa da kasa, kana ya umurci ma’aikatar tsaro ta Amurka, da ta shirya wajen daukar matakin soji a Najeriya idan hakan ya zama wajaba.

To ko me ya sa Amurka ta sa hannu cikin harkokin gidan Najeriya ba zato ba tsammani? Kuma ko mene ne ainihin burinta?

Lallai, Amurka tana zargin Nijeriya da “cin zarafin Kiristoci a Najeriya”, amma gaskiyar lamarin shi ne, mafi yawan rikice-rikice da ke faruwa a Najeriya suna da alaka da kwaton albarkatu da rikice-rikicen kabilu, yayin da kungiyar masu tsattsauran ra’ayi ta “Boko Haram”, ke kai hare-hare ba tare da bambanta wani addini ba. Ko musulmai ma suna cikin wadanda abin ya fi shafa. Don hakan zargin na “kisan kiyashi na addini” ba shi da tushe balle makama.

ADVERTISEMENT

A bangaren siyasar cikin gidan Amurka, shugaba Trump yana amfani da “kare mabiyan addinin Kirista” don neman gamsar da masu jefa masa kuri’a mabiyan addinin kirista ‘yan bushara, don samun goyon bayansu, tare da dora laifi kan saura game da matsalolin tattalin arziki da rashin aikin yi a cikin Amurka.

A fannin tattalin arziki kuma, Najeriya a matsayinta na kasar da ta fi yawan samar da mai a Afirka, Amurka ta matsawa Najeriya lamba ne da nufin mallakar makamashinta da sauran muhimman albarkatu, tare da raunana tasirin wasu kasashe a fannin hadin gwiwar makamashi tsakaninsu da Najeriya.

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

A sa’i daya kuma, Najeriya muhimmiyar kasa ce a yankin yammacin Afirka. Amurka na neman shiga fagen tsaron Najeriya ne ta hanyar fakewa da batun “hadin gwiwar tsaro”, don dakile yunkurin adawa da kasashen yamma a yammacin Afirka, tare da tilasta wa Najeriya nuna goyon bayanta.

Sai kuma ta fannin dangantakar Najeriya da Amurka, game da harajin da Amurka ta kakabawa sassa daban daban, shugaban Najeriyar Bola Tinubu ya taba cewa: “Idan kudaden shigarmu da ba na bangarorin mai ba suna karuwa, ba za mu ji tsoron duk wani abu da Trump ke yi ba.” Kazalika, a babban taron MDD na karo na 80, mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima ya zargin matakan da Isra’ila ta dauka a Gaza, da kuma asarar rayukan Palasdinawa da hakan ya haifar. Hakan ne ma ya sanya kafofin yada labarai na Amurka, suka karawa labaran tashe-tashen hankula na cikin gidan Najeriya gishiri, don mai da martani ga Najeriya kan wadannan batutuwa.

A duniyar yau, yawancin kasashe suna mayar da hankali kan zaman lafiya da ci gaba, suna kara hadin gwiwa don cin moriya tare. Irin wannan dabaru da Amurka ke dauka na yin barazana, da matsin lamba, da sanya takunkumi bisa karfinta sam ba su dace ba. Dole ne ‘yan Najeriya su jagoranci kansu, su magance matsalolin Najeriya da karfin kansu. Kamata ya yi Amurka ta daina sa hannu cikin harkokin cikin gidan Najeriya. (Mai rubutu: MINA)

Amurka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Faransa 

Xi Jinping Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Faransa 

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.