ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Amurka Ta Daina Sa Hannu Cikin Harkokin Najeriya

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
Amurka

Bisa labarin da jaridar ‘The Punch’ ta Najeriya ta bayar, an ce, a kwanan nan kwamitocin majalisar dokokin Amurka sun gudanar da taro, don tantance lamuran garkuwa da mutane da ke faruwa a Najeriya, da kuma batun zargin da aka yi cewa wai ana cin zarafin Kiristoci a kasar. Kafin hakan, shugaban Amurka Donald Trump ya furta a shafinsa na sada zumunta cewa, Najeriya ta zama “wuri mai barazana ga rayuwar mabiyan addinin Kirista”, ya kuma sake sanya Najeriya a cikin jerin kasashe da ake sa musu kulawar musamman bisa dokar ‘yancin addini ta kasa da kasa, kana ya umurci ma’aikatar tsaro ta Amurka, da ta shirya wajen daukar matakin soji a Najeriya idan hakan ya zama wajaba.

To ko me ya sa Amurka ta sa hannu cikin harkokin gidan Najeriya ba zato ba tsammani? Kuma ko mene ne ainihin burinta?

Lallai, Amurka tana zargin Nijeriya da “cin zarafin Kiristoci a Najeriya”, amma gaskiyar lamarin shi ne, mafi yawan rikice-rikice da ke faruwa a Najeriya suna da alaka da kwaton albarkatu da rikice-rikicen kabilu, yayin da kungiyar masu tsattsauran ra’ayi ta “Boko Haram”, ke kai hare-hare ba tare da bambanta wani addini ba. Ko musulmai ma suna cikin wadanda abin ya fi shafa. Don hakan zargin na “kisan kiyashi na addini” ba shi da tushe balle makama.

ADVERTISEMENT

A bangaren siyasar cikin gidan Amurka, shugaba Trump yana amfani da “kare mabiyan addinin Kirista” don neman gamsar da masu jefa masa kuri’a mabiyan addinin kirista ‘yan bushara, don samun goyon bayansu, tare da dora laifi kan saura game da matsalolin tattalin arziki da rashin aikin yi a cikin Amurka.

A fannin tattalin arziki kuma, Najeriya a matsayinta na kasar da ta fi yawan samar da mai a Afirka, Amurka ta matsawa Najeriya lamba ne da nufin mallakar makamashinta da sauran muhimman albarkatu, tare da raunana tasirin wasu kasashe a fannin hadin gwiwar makamashi tsakaninsu da Najeriya.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

A sa’i daya kuma, Najeriya muhimmiyar kasa ce a yankin yammacin Afirka. Amurka na neman shiga fagen tsaron Najeriya ne ta hanyar fakewa da batun “hadin gwiwar tsaro”, don dakile yunkurin adawa da kasashen yamma a yammacin Afirka, tare da tilasta wa Najeriya nuna goyon bayanta.

Sai kuma ta fannin dangantakar Najeriya da Amurka, game da harajin da Amurka ta kakabawa sassa daban daban, shugaban Najeriyar Bola Tinubu ya taba cewa: “Idan kudaden shigarmu da ba na bangarorin mai ba suna karuwa, ba za mu ji tsoron duk wani abu da Trump ke yi ba.” Kazalika, a babban taron MDD na karo na 80, mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima ya zargin matakan da Isra’ila ta dauka a Gaza, da kuma asarar rayukan Palasdinawa da hakan ya haifar. Hakan ne ma ya sanya kafofin yada labarai na Amurka, suka karawa labaran tashe-tashen hankula na cikin gidan Najeriya gishiri, don mai da martani ga Najeriya kan wadannan batutuwa.

A duniyar yau, yawancin kasashe suna mayar da hankali kan zaman lafiya da ci gaba, suna kara hadin gwiwa don cin moriya tare. Irin wannan dabaru da Amurka ke dauka na yin barazana, da matsin lamba, da sanya takunkumi bisa karfinta sam ba su dace ba. Dole ne ‘yan Najeriya su jagoranci kansu, su magance matsalolin Najeriya da karfin kansu. Kamata ya yi Amurka ta daina sa hannu cikin harkokin cikin gidan Najeriya. (Mai rubutu: MINA)

Amurka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Faransa 

Xi Jinping Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Faransa 

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.