• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Buhari Ya Dakile Barazanar Da APC Ke Fuskanta A Majalisar Dattawa

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Buhari Ya Ce Ba Zai Nemi Wa’adi Na Uku Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu ‘yan majalisar dattawa na jam’iyyar APC guda 22 sun yi barazanar sauya sheka zuwa jam’iyyun PDP da LP da NNPP da dai sauran su, bisa kara fusatasu da aka yi sakamakon zaben fid da gwani da aka kammala.

Ganin haka ne ma ya sa Shugaban Kasa Muhammadu Buhari a ranar Talata ya roki sanatocin na APC kan kar su bar jam’iyyar domin kar ta rasa rinjaye a zauren majalisan dattawan Nijeriya.

  • 2023: Bayan Buhari, Dole Dan Kudu Ya Zama Shugaban Kasa – Fayose

Shugaba Buhari ya samu zama da wasu ‘yan majalisan dattawa na APC domin jin irin matsalolin da aka samu a wurin zaben fid da gwani da aka kammala. Ya dai amshi korafinsu tare da tabbatar da cewa kwamitin gudanarwa na jam’iyyar za ta bi ba’asi a kan lamarin.

Ya bukaci ‘yan majalisan da su ci gaba da kokarinsu wajen ganin shugabancin jam’iyyar APC ya bunkasa kasar nan.

Ya ce, “Na ji dukkan korafe-korafenku kan zaben fid da gwani da aka kammala, zan yi kokarin ganin an share wa kowa hawayensa domin jam’iyyarmu ta ci gaba da iko a zauren majalisan dattawa da kuma babban zaben 2023. Ba za mu taba barin wannan barazanar ba tabbata ba.
“Akwai hanyoyin da za mu bi wajen warware duk wata matsa da ta kunno kai.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

Wannan shi ne kyakkywan tsari a cikin dimokuradiyyarmu wanda muke gudanarwa. Tun daga lokacin da aka kammala zaben fid da gwani nake ta samun rahoto na korafe-korafe,” in ji shi.

A cewar mashawarcin shugaban kasa a fannin yada labarai, Femi Adesina, Shugaba Buhari ya sha alwashin karfafa shugabancin jam’iyyar APC ta hanyar yin adalci a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar kafin babban zaben 2023.

Shugaba Buhari ya fada wa sanatocin APC cewa samun nasarar jam’iyyar a babban zabe ya ta’allaka ne da yanayin hadin kan ‘ya’yan jam’iyyar da kaucewa rashin adalci a tsakaninsu.

Sai dai kuma Buhari ya gode wa ‘yan majalisan dattawan bisa bayar da shawaran gudanar da tattaunawa ta yadda za a su damar dinke bakin zaren na matsaloli da suka faru a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar a lokacin zaben fid da gwani.

A nasa jawabin, shugaban tawagan kuma babban mai tsawatarwa na majalisar dattawa, Sanata Orji Uzor Kalu, ya bayyana cewa a yanzu haka akwai a kalla sanatoci 22 da wasu mambobi na jam’iyyar ba su ji dadin abubuwan da suka faru a zaben fid da gwani da aka kammala ba a jihohinsu ba, saboda an gudanar da wasu lamari ba bisa ka’ida ba, wanda suka yi barazanar sauya sheka zuwa wasu jam’iyyun na daban.

Ya kara da cewa ‘yan majalisan dattawan sun sadaukar da kawunansu wajen ganin jam’iyyar ta bunka a cikin dimokuradiyyar kasar nan. Ya yi kira da shugaban kasa ya kawo daukin gaggawa kan wannan lamari.

Ya ce, “Mai girma shugaban kasa, tabbas a zauren majalisa mun yi aiki tukuru wajen ganin duk manufofinka sun gudana. Muna tabbatar maka da cewa a ko da yaushe muna goyon bayanka,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Tinubu Da Atiku Ba Za Su Iya Gyara Nijeriya Ba — Ango Abdullahi

Next Post

Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabi Yayin Bikin Cika Shekaru 25 Da Dawowar HK Kasar Sin Da Na Kaddamar Da Sabuwar Gwamnatin Yankin

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

2 weeks ago
Buhari
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

2 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

2 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

3 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

3 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

3 weeks ago
Next Post
Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabi Yayin Bikin Cika Shekaru 25 Da Dawowar HK Kasar Sin Da Na Kaddamar Da Sabuwar Gwamnatin Yankin

Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabi Yayin Bikin Cika Shekaru 25 Da Dawowar HK Kasar Sin Da Na Kaddamar Da Sabuwar Gwamnatin Yankin

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.