• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Hukuncin Kotun Koli Ya Kara Dagula Rikicin Shugabanci A PDP Da LP

by Yusuf Shuaibu
3 weeks ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Shari’ar Zaben Gwamnoni: Kallo Ya Koma Kotun Koli
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duk da hukuncin kotun kolin Nijeriya, rikicin shugabanci da ya dabaibaye jam’iyyar PDP da LP ya kara kamari, a halin da ake ciki har yanzu jam’iyyun guda biyu sun gaza magance rikicin shugabanci.

Duk da cewa shugabannin jam’iyyun biyu sun yaba da hukuncin kotun koli wanda a cikin hukunce-hukuncen daban-daban, har yanzu jam’iyyun biyu ba su sami masalaha ba game da warware rikicin cikin gida a tsakaninsu.

  • Manchester Ta Kai Zagayen Semi Final A Europa Bayan Doke Lyon
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 157, Sun Ƙwato Bindigu Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Yayin da jam’iyyar PDP ke fama game da rikicin sakataren jam’iyyar na kasa, inda jam’iyyar LP ke fama da rikicin shugabanta na kasa.

Mutane uku na ikirarin zama shugabannin LP, yayin da Sanata Samuel Anyanwu da Hon. Sunday Udeh-Okoye ke fafatawa kan wane ne ainihin sakataren PDP na kasa.

A cikin LP, Kwamared Julies Abure ya ci gaba da rike sakatariyar jam’iyyar, yayin da Sanata Nenadi Usman da Lamidi Apapa suma ke ikirarin zama shugabannin jam’iyyar.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

Wata majiya ta ce PDP na cikin mawuyacin hali da kuma rashin tabbas a harkokinta wanda ya tilasta jinkirta taron shiyya da aka shirya gudanarwa a karshen makon da ya gabata.

Wata majiya ta ce hukuncin da kotun koli ta zartar akwai rikitarwa saboda an gwama siyasa a ciki.

Amma sakataren yada labarai na jam’iyyar PDP na kasa, Debo Ologunagba ya fada a wata hira kan cewa hukuncin kotun koli a bayyane yake kuma yana da fa’ida ga gudanar da jam’iyyar a kasar, ya kara da cewa an ba da ikon magance matsalolin da ke tattare da rikice-rikicen da za su iya shafi masu rike da mukaman jam’iyyar.

Ya ce abin da kotun ta yanke hukunci shi ne cewa dole ne a warware duk wani abu da ya shafi matsayi na jam’iyya ta hanyar tsarin cikin gida na jam’iyya, sannan kotun ta ce ba za ta yi katsalandan ga al’amuran jam’iyyu ba kamar yadda dokoki da ka’idoji suka bayyana.

Ya ce PDP ba ta cikin wani mawuyacin hali game da hukuncin, ya kara da cewa tsarin cikin gida na jam’iyyar zai yanke shawara tare da samar da mafita.

Yayin da PDP tana cikin mawuyacin hali saboda jinkirin warware matsayin sakataren jam’iyyar na kasa, al’amura na kara tabarbarewa a LP. A makon da ya gabata ne bangare uku suke ikirarin zama shugabannin jam’iyyar na kasa.

Julius Abure, Nenadi Usman da Lamidi Apapa sun ci gaba ikirarinsu na zama a matsayin shugabancin jam’iyyar, duk da cewa sakataren yada labarai na kasa, Obiora Ifoh, ya bayyana cewa wadanda ke fafatawa da Abure suna yin was an kwaikoyo ne kawai.

A cewarsa, a yayin da kotun koli ta fadi karara cewa ba ta da iko a kan lamarin da ya shafi rikicin cikin gida na jam’iyya kuma ta mayar da iko ga tsarin jam’iyyar, wasu mambobin jam’iyyar suna yin wasan kwaikwayo ta hanyar zuwa ofishin hukumar zabe ta kasa, lamarin da ya ce ba shi da tasiri.

Ya ce hukuncin kotun koli ya yi watsi da batun shugabancin jam’iyyar tare da soke hukuncin kotun daukaka kara, har ma ba ta tabbatar da wani mutum a matsayin shugaban jam’iyyar ba.

“Abin da wannan ke nufi shi ne, an mayar da jam’iyyar zuwa matsayi na farko. Kuma Abure ya kasance shugaban jam’iyyar na kasa har tsawon lokacin da wa’adinsa ya kare,” in ji Ifoh.

Mai magana da yawun jam’iyyar ya gargadin Sanata Nenadi Usman da sauran masu adawa da Abure cewa kar su yaudari ‘yan Nijeriya da fassarar da ba daidai ba game da hukuncin kotun koli.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dan Takarar Gwamnan PDPHukunciKotun ƘoliLPPDP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Nemi Kasashen Duniya Su Taimaka Wa Libya Wajen Fita Daga Kangin Da Take Ciki

Next Post

Kasar Sin Ta Mallaki Tasoshin Fasahar 5G Miliyan 4.4 A Halin Yanzu

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

7 days ago
Kotun
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

7 days ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

7 days ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

2 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

2 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

2 weeks ago
Next Post
Kasar Sin Ta Mallaki Tasoshin Fasahar 5G Miliyan 4.4 A Halin Yanzu

Kasar Sin Ta Mallaki Tasoshin Fasahar 5G Miliyan 4.4 A Halin Yanzu

LABARAI MASU NASABA

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.