ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

by Sulaiman
5 months ago
Noma

A Jihar Kaduna, wasu manoma masu fama da nakasa daban-daban kama daga makafi da Guragu da kuma kurame sun rungumi dabarun noman zamani don tallafawa kansu.

Wadannan nakasassun manoma suna gudanar da aikin noma ne ta tsarin da aka fi sani da “Inclusibe Farming System for Persons with Disabilities To Fight Hunger in Nigeria ,” wanda ke da nufin shigar da kowa musamman masu nakasa wajen noma domin yakar yunwa a Nijeriya.

  • WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe
  • NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

A halin yanzu, nakasassun manoma sun himmatu wajen aikin noma a matsayin hanyar ciyar da kansu, maimakon barace-barace.

ADVERTISEMENT

Duk da karancin ruwan sama a bana, manoman ba su yi kasa a gwiwa ba; suna ci gaba da yin aiki tukuru a gonakinsu, ta hanyar amfani da dabarun zamani don tabbatar da samar da wadataccen abinci mai inganci.

A Jihar Kaduna masu bukata ta musamman sun kama hanyar zama gwarazan manoma, sakamakon yadda da dama daga cikin masu nakasa suka mayar da hankali kan noman zamani a jihar domin inganta rayuwarsu.

LABARAI MASU NASABA

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

Wannan yana cikin wani tsari na noma da aka kirkiro musamman don masu bukata ta musamman domin su dogara da kansu maimakon rokon hatsi ko neman taimako.

Wannan yana cikin wani tsari na noma da aka kirkiro musamman don masu bukata ta musamman domin su dogara da kansu maimakon rokon hatsi ko neman taimako.

Wakilinmu ya ziyarcj wata kebabbiyar gona dake cikin garin Kaduna, inda gungun wasu manoma da ke fama da lalurori daban-daban irin su makanta da gurguntaka da kurma, suka rungumi sabbin dabarun noma na zamani domin tallafawa rayuwarsu, musamman a wannan damina da aka shiga.

Gonakin da wadanda makafi da guragu ne suke nomawa a duk shekara Sun bayyana cewa suna gudanar da nomansu ne ba tare da wata gudummawa daga gwamnati ba kama da samar musu da takin zamani da sauran kayan noma kamar yadda ake tallafawa Masu lafiya.

A zantawarsa da wakilinmu a cikin gonarsa, Mista William Makiya, wanda ke fama da matsalar gani (makaho), yana noma da huda domin ciyar da iyalinsa. Ya bayyana cewa:

“Ba na gani da idona. Dalilin da yasa nake yin noma shine domin ciyar da iyalina. Ba na yin bara kuma bana san yin bara kwata-kwata rayuwata. Ba na kaunar bara.”

William ya kara da cewa yana jin dadin aikin noma, kuma yana taimakawa makwabtansa masu lafiya da kayan abinci daga gonarsa. Wannan yana karfafa zumunci da hadin kai tsakaninsa da sauran al’umma da suke zaune tare a cikin muhalli daya.

Ya ce:“Da galma nake yin wannan noma. Ina amfani da fatanya da sauran kayan huda wajen noma da kuma cire ciyawa a gonaki.”

Ya ci gaba da cewa gonarsa tana da layukan shuka wanda yake amfani da su wajen shuka wake, dankalin hausa, gyada, da kayan lambu irin su tumatur da kubewa.

A kowace shekara, jajirtattun manoma masu bukata ta musamman ne ke amfani da wadannan filayen noma domin ciyar da kansu, kamar yadda wani matashi mai lalurar kafa Mai Suna Joshua Matthew, ya bayyana cewa Shi ma yana noma da huda a gonarsa.

“Abin da ya kamata a sani shi ne, ni ina noma da huda sosai domin ciyar da iyalina. Ina noma masara da shinkafa da sauran kayayyakin abinci domin rage tsadar rayuwa.”

Joshua ya ce duk da cewa ba shi da kafa, yana zaune yana jan jikinsa domin yin noma da cire ciyawa da sauran ayyukan noma. Ya tabbatar da cewa ya dade yana wannan aiki, kuma babu wahala kamar yadda mutane ke tunani.

Ya jaddada bukatar gwamnati ta tallafa musu domin su zama masu dogaro da kansu.

Duk da karancin ruwan sama a bana, wadannan manoma ba su karaya ba. Sun ci gaba da aiki tukuru a gonakinsu, suna amfani da dabarun noma na zamani domin tabbatar da samun abinci mai yawa da inganci.

Babu shakka, wadannan manoma suna gudanar da aikin noma ta hanyar wani tsarin hada kowa da kowa musamman masu nakasa cikin harkar noma domin yakar yunwa da talauci a Nijeriya. Wannan tsarin na “inclusibe smart farming” ya fara haifar da nasarori, a cewar Kwamared Rilwani Abdullahi, shugaban kungiyar masu bukata ta musamman a Nijeriya.

Ya ce:“Wannan wani yunkuri ne na zama masu dogaro da kai. Saboda haka, muna kira ga hukumomi da su tashi tsaye wajen tallafawa wadannan manoma, da kuma tabbatar da cewa ana sanya su a cikin jerin manoman da ake tallafawa a duk lokacin da ake rabon takin zamani.”

Yanzu haka dai, wadannan gwarazan manoma sun dukufa sosai cikin harkar noma domin ciyar da kansu maimakon barace-barace. Sai dai, sun koka kan yadda ake rarraba takin zamani ba tare da an tuna da su ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace
Rahotonni

Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

December 20, 2025
Tinubu Ya Nuna Kwarewa Da Gogewa A Sha’anin Mulkin Nijeriya – Bishir Dauda
Rahotonni

Tinubu Ya Nuna Kwarewa Da Gogewa A Sha’anin Mulkin Nijeriya – Bishir Dauda

December 19, 2025
Next Post
‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.