• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Mutanen Buhari Suka Sha Kaye A Zaben Fitar Da Gwanin APC A Kano

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Wata Budurwa ‘Yar Shekara 28 Ta Kayar Da Dan Majalisa A Zaben Fidda Gwani Na APC A Inugu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsofaffin mataimaka na musamman ga Shugaban Kasa Muhammadu Buhari wadanda suka tsaya takara a jam’iyyar APC na neman kujerar gwamna da majalisar dattawa da na majalisar wakilai a Jihar Kano dukkan su sun sha kaye a zaben fitar da gwani.

Sun dai hada da Sha’aban Sharada, wanda shi ne tsohon mataimaki na musam-man ga shugaban kasa kan watsa labarai, wanda a halin yanzu haka shi ne shuga-ban kwamitin majalisar wakilai kan fasahar tsaron kasa da tsohon mataimaki na musamman kan kafafen yada labarai na zamani, Bashir Ahmad da kuma tsohon mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan bunkasa zamantakewa, Ismaeel Ahmed duk sun sha kaye a zaben fitar da gwani da ya gabata a Jihar Kano.

  • Kamfanonin Kasar Sin Sun Ba Da Kyauta Ga Daliban Ghana Da Ke Fama Da Talauci

Sun dai sha kayen ne a hannun ‘yan takarar da Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya mara wa baya.

Shi dai Sha’aban ya tsaya takarar gwamna ne a karkashin jam’iyyar, yayin da Bashir ya nemi samun tikitin takarar dan majalisa na mazanar Albasu/Gaya/Ajingi, sai kuma Ismaeel da ya nemi tikitin takarar dan majalisar dattawa na Kano ta tsakiya.

Ismaeel ya bayyana janyewar takararsa mintina kadan kafin gudanar da zaben fitar da gwani. Amma shi Sha’aban da kuma Bashir an gudanar da zaben fitar da gwanin da su wadanda suka sha kaye.
Bayanai dai sun nuna cewa, Ismaeel ya janye takararsa ne bayan da gwamna ya tabbatar masa da cewa Abdulsalam Abdulkarim Zaura zai bai wa tikitin takara.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Sha’aban dai ya samu kuri’u 30, yayin da abokin karawarsa mataimakin gwamna, Nasiru Yusuf Gawuna wanda ya lashe zaben ya samu kuri’u 2,289.

Bashir dai ya samu kuri’a 16, yayin da abokin karawarsa da ya lashe zaben, Abdul-lahi Mahmoud Gaya ya samu kuri’u 109.

Masu sharhi kan zaben Kano sun bayyana cewa sakamakon zaben fitar da gwani na takarar gwamnan bai zo da mamaki ba, saboda Sha’aban yana takun-saka da gwamna da kuma shugabannin jam’iyyar APC na jihar tun a shekarar 2021.

Shi kuma Bashir a tunaninsa zai iya samun tikitin takarar dan majalisar wakilai ci-kin ruwan sanyi tun da dai ya kasance yaro ne ga fadar shugaban kasa kamar dai abokinsa Sha’aban, amma bai yi nasara ba.

Majiyar ta tabbatar da cewa, lokacin da Bashir ya bayyana wa shugaban kasa a niyarsa ta tsayawa takara ya amince da bukatarsa kamar dai sauran ‘yan takara da suka bayyana masa aniyarsu. Amma kuma hakan bai hana shi shan kaye ba.

Shi dai Bashir ya zargi shugabannin jam’iyyar a jihar da yin masa magudi a zaben, inda ya yi zargin an yi amfani da ‘yan daba a kansa da kuma magoya bayansa wajen tursasa musu barin wurin zaben.

Masu saka ido a zaben sun bayyana cewa bayan rashin gogewa a siyasar mazaba, babban abin da ya sa mutanen Buhari suka sha kaye shi ne, shugaban kasa bai nuna sha’awa a cikin takararsu ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Nijeriya Na Gaba Zai Kashe Kudaden Haraji Ne Kan Biyan Bashi –IMF

Next Post

Jam’iyyar ZLP Ta Tsayar Da Dan Takarar Gwamna A Jihar Kano

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

2 weeks ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

2 weeks ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

2 weeks ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

3 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

3 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

3 weeks ago
Next Post
Jam’iyyar ZLP Ta Tsayar Da Dan Takarar Gwamna A Jihar Kano

Jam'iyyar ZLP Ta Tsayar Da Dan Takarar Gwamna A Jihar Kano

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.