• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Noman Shanu Ya Rage Amfanin Gonar Da Ake Samu A Kaduna

by Abubakar Abba
10 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Yadda Noman Shanu Ya Rage Amfanin Gonar Da Ake Samu A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kashi 90 na manoman Karamar Hukumar Kudan a Jihar Kaduna, na amfani da Garmar Shanu ne, wajen gyaran gonakinsu tare kuma da rashin samun kwararrun masu yin aikin, wanda hakan ya jawo rashin noma amfanin gona mai yawa.

An gano hakan ne, biyo bayan binciken da tawagar sa ido a fannin aikin noma tare da wata kungiya mai zaman kanta ‘PYDERA Global’ suka yi a karkashin shirin kungiykr na Rayuwa.

  • Tura Ta Kai Bango, Zanga-zanga Ta Kai Gidan Buhari Da Sarkin Daura
  • An Tarwatsa Masu Zanga-zanga Kan Kokarin Kunna Wuta A Kofar Gidan Gwamnatin Kano

Kwararre a aikin noma a karkashin shirin, Mista Nathaniel Otene; yayin da yake rabar da injinonin Garma na zamani guda 15 ga manoman da ke Kudan kuma da na Karamar Hukumar Kafur ta Jihar Katsina.

Ya ce, yin amfani da Garmar Shanu wajen yin noma; na jawo wa kananan manoma rashin samun kudaden shiga masu yawa, inda ya kara da cewa, don rage kalubalen rashin wadataccen abinci da kuma habaka tattalin arziki, musamman na kananan manoma; ya sa kungiyar ta wanzar da wannan shiri nata na Rayuwa, ta hanyar raba wa manoman injinon Garmar na zamani guda 15, domin yin noma.

A cewar Otene, wadannan kaya; ko shakka babu za su taimaka wa manoman da suka amfana wadannan injina matuka wajen gyara gonakinsu da kuma kara samar musu da kudaden shiga.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

Ya kara da cewa, an zabo manoman da suka amfana da wannan tallafi ne daga cikin kungiyoyi daban-daban, bisa tsarin ba su wannan tallafi.

Ya sanar da cewa, kimanin manoma 375 ne da suka fito daga Kananan Hukumomin Kudan ta Jihar Kaduna da kuma wasu 200 daga Karamar Hukumar Kafur ta Jihar Katsina.

A jawabinsa a wajen rabar da kayan, Shugaban Karamar Hukumar Kudan, Shuaibu Bawa Jaja; ya yaba wa kungiyar a kan rabar da wadannan kaya tare da yin kira ga kungiyar da taimaka wa sauran kananan manoman da ba su samu damar amfana da kayan a wannan karon ba.

Shi ma, a nasa jawabin Dagacin Kudan; Alhaji Halliru Mahmood da kuma Dagacin Hunkuyi, Alhaji Aminu Ashiru; sun yi kira ga wadanda suka amfanan da kayan da su yi amfani da su ta hanyar da ta dace tare kuma da taimaka wa wadanda ba su samu ba, domin gyara nasu gonakin su ma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GonakiKadunaNomaShanu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Dattawa Ta Bukaci NEMA Ta Kai Wa Manoman Citta Dauki A Kaduna

Next Post

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Ya Kamata Amurka Ta Gyara Kurakuran Da Ta Tafka Wajen Keta Hakkin Dan Adam A Duniya

Related

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

4 days ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

4 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

4 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

2 weeks ago
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

3 weeks ago
Next Post
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Ya Kamata Amurka Ta Gyara Kurakuran Da Ta Tafka Wajen Keta Hakkin Dan Adam A Duniya

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Ya Kamata Amurka Ta Gyara Kurakuran Da Ta Tafka Wajen Keta Hakkin Dan Adam A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

June 4, 2025
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

June 3, 2025
Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun GargaÉ—i Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

June 3, 2025
An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

June 3, 2025
Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

June 3, 2025
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.