• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Noman Shanu Ya Rage Amfanin Gonar Da Ake Samu A Kaduna

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Yadda Noman Shanu Ya Rage Amfanin Gonar Da Ake Samu A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kashi 90 na manoman Karamar Hukumar Kudan a Jihar Kaduna, na amfani da Garmar Shanu ne, wajen gyaran gonakinsu tare kuma da rashin samun kwararrun masu yin aikin, wanda hakan ya jawo rashin noma amfanin gona mai yawa.

An gano hakan ne, biyo bayan binciken da tawagar sa ido a fannin aikin noma tare da wata kungiya mai zaman kanta ‘PYDERA Global’ suka yi a karkashin shirin kungiykr na Rayuwa.

  • Tura Ta Kai Bango, Zanga-zanga Ta Kai Gidan Buhari Da Sarkin Daura
  • An Tarwatsa Masu Zanga-zanga Kan Kokarin Kunna Wuta A Kofar Gidan Gwamnatin Kano

Kwararre a aikin noma a karkashin shirin, Mista Nathaniel Otene; yayin da yake rabar da injinonin Garma na zamani guda 15 ga manoman da ke Kudan kuma da na Karamar Hukumar Kafur ta Jihar Katsina.

Ya ce, yin amfani da Garmar Shanu wajen yin noma; na jawo wa kananan manoma rashin samun kudaden shiga masu yawa, inda ya kara da cewa, don rage kalubalen rashin wadataccen abinci da kuma habaka tattalin arziki, musamman na kananan manoma; ya sa kungiyar ta wanzar da wannan shiri nata na Rayuwa, ta hanyar raba wa manoman injinon Garmar na zamani guda 15, domin yin noma.

A cewar Otene, wadannan kaya; ko shakka babu za su taimaka wa manoman da suka amfana wadannan injina matuka wajen gyara gonakinsu da kuma kara samar musu da kudaden shiga.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya kara da cewa, an zabo manoman da suka amfana da wannan tallafi ne daga cikin kungiyoyi daban-daban, bisa tsarin ba su wannan tallafi.

Ya sanar da cewa, kimanin manoma 375 ne da suka fito daga Kananan Hukumomin Kudan ta Jihar Kaduna da kuma wasu 200 daga Karamar Hukumar Kafur ta Jihar Katsina.

A jawabinsa a wajen rabar da kayan, Shugaban Karamar Hukumar Kudan, Shuaibu Bawa Jaja; ya yaba wa kungiyar a kan rabar da wadannan kaya tare da yin kira ga kungiyar da taimaka wa sauran kananan manoman da ba su samu damar amfana da kayan a wannan karon ba.

Shi ma, a nasa jawabin Dagacin Kudan; Alhaji Halliru Mahmood da kuma Dagacin Hunkuyi, Alhaji Aminu Ashiru; sun yi kira ga wadanda suka amfanan da kayan da su yi amfani da su ta hanyar da ta dace tare kuma da taimaka wa wadanda ba su samu ba, domin gyara nasu gonakin su ma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GonakiKadunaNomaShanu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Dattawa Ta Bukaci NEMA Ta Kai Wa Manoman Citta Dauki A Kaduna

Next Post

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Ya Kamata Amurka Ta Gyara Kurakuran Da Ta Tafka Wajen Keta Hakkin Dan Adam A Duniya

Related

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

21 hours ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

22 hours ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

1 week ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

1 week ago
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

2 weeks ago
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
Noma Da Kiwo

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

2 weeks ago
Next Post
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Ya Kamata Amurka Ta Gyara Kurakuran Da Ta Tafka Wajen Keta Hakkin Dan Adam A Duniya

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Ya Kamata Amurka Ta Gyara Kurakuran Da Ta Tafka Wajen Keta Hakkin Dan Adam A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.