ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Noman Shanu Ya Rage Amfanin Gonar Da Ake Samu A Kaduna

by Abubakar Abba
2 years ago
Shanu

Kashi 90 na manoman Karamar Hukumar Kudan a Jihar Kaduna, na amfani da Garmar Shanu ne, wajen gyaran gonakinsu tare kuma da rashin samun kwararrun masu yin aikin, wanda hakan ya jawo rashin noma amfanin gona mai yawa.

An gano hakan ne, biyo bayan binciken da tawagar sa ido a fannin aikin noma tare da wata kungiya mai zaman kanta ‘PYDERA Global’ suka yi a karkashin shirin kungiykr na Rayuwa.

  • Tura Ta Kai Bango, Zanga-zanga Ta Kai Gidan Buhari Da Sarkin Daura
  • An Tarwatsa Masu Zanga-zanga Kan Kokarin Kunna Wuta A Kofar Gidan Gwamnatin Kano

Kwararre a aikin noma a karkashin shirin, Mista Nathaniel Otene; yayin da yake rabar da injinonin Garma na zamani guda 15 ga manoman da ke Kudan kuma da na Karamar Hukumar Kafur ta Jihar Katsina.

ADVERTISEMENT

Ya ce, yin amfani da Garmar Shanu wajen yin noma; na jawo wa kananan manoma rashin samun kudaden shiga masu yawa, inda ya kara da cewa, don rage kalubalen rashin wadataccen abinci da kuma habaka tattalin arziki, musamman na kananan manoma; ya sa kungiyar ta wanzar da wannan shiri nata na Rayuwa, ta hanyar raba wa manoman injinon Garmar na zamani guda 15, domin yin noma.

A cewar Otene, wadannan kaya; ko shakka babu za su taimaka wa manoman da suka amfana wadannan injina matuka wajen gyara gonakinsu da kuma kara samar musu da kudaden shiga.

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

Ya kara da cewa, an zabo manoman da suka amfana da wannan tallafi ne daga cikin kungiyoyi daban-daban, bisa tsarin ba su wannan tallafi.

Ya sanar da cewa, kimanin manoma 375 ne da suka fito daga Kananan Hukumomin Kudan ta Jihar Kaduna da kuma wasu 200 daga Karamar Hukumar Kafur ta Jihar Katsina.

A jawabinsa a wajen rabar da kayan, Shugaban Karamar Hukumar Kudan, Shuaibu Bawa Jaja; ya yaba wa kungiyar a kan rabar da wadannan kaya tare da yin kira ga kungiyar da taimaka wa sauran kananan manoman da ba su samu damar amfana da kayan a wannan karon ba.

Shi ma, a nasa jawabin Dagacin Kudan; Alhaji Halliru Mahmood da kuma Dagacin Hunkuyi, Alhaji Aminu Ashiru; sun yi kira ga wadanda suka amfanan da kayan da su yi amfani da su ta hanyar da ta dace tare kuma da taimaka wa wadanda ba su samu ba, domin gyara nasu gonakin su ma.

Shanu
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Ɗaura Ɗamarar Magance Matsalolin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

MASU ALAKA

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 
Noma Da Kiwo

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

June 27, 2026
Next Post
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Ya Kamata Amurka Ta Gyara Kurakuran Da Ta Tafka Wajen Keta Hakkin Dan Adam A Duniya

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Ya Kamata Amurka Ta Gyara Kurakuran Da Ta Tafka Wajen Keta Hakkin Dan Adam A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

July 10, 2026
NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

“Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

July 10, 2026
Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

July 10, 2026
Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu

Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu

July 10, 2026
Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisar Kan Gyaran Kudirin Dokar Shari’ar Manyan Laifuka

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisar Kan Gyaran Kudirin Dokar Shari’ar Manyan Laifuka

July 10, 2026
Taƙaddamar Kafa Hukumar Bogi: Tinubu Ya Umarci A Yi Binciken Ƙwaƙwaf

Taƙaddamar Kafa Hukumar Bogi: Tinubu Ya Umarci A Yi Binciken Ƙwaƙwaf

July 10, 2026
Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

July 10, 2026
Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin

Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin

July 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.