• English
  • Business News
Thursday, August 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Rangers Ta Lashe Gasar Firimiyar Nijeriya 

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
in Wasanni
0
Yadda Rangers Ta Lashe Gasar Firimiyar Nijeriya 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kawo yanzu dai kungiyar kwallon kafa ta Enugu Rangers ta lashe kofin babbar gasar firimiyar Nijeriya a karo na takwas bayan doke kungiyar kwallon kafa ta Gombe United har gida da ci 2-1.

Rangers ta samu jimillar maki 70 a gasar ta Nijeriya Professional Footbal League (NPFL) kakar wasa ta 2023 zuwa 2024, wanda hakan ke nufin ta samu tikitin zuwa gasar Zakarun Afirka na shekara mai zuwa.

  • Barazanar Da Rashin Katabus Na Kananan Hukumomi Ke Yi Ga Dimokuradiyyar Nijeriya
  • Yadda Aka Yi Bikin Kaddamar Da Littafin Babban Editan LEADERSHIP A Abuja

An gudanar da bikin ba ta kofin ne a filin wasa na Jos International Stadium – inda Gombe United ke buga wasanninta na gida kuma bayan wasannin mako na 38 kamar yadda yake a doka.

Kungiyar Rangers ce ta fara cin kwallo minti uku da fara wasa ta hannun dan wasa Ogunleye, sannan Obaje ya kara minti hudu bayan haka, kafin Hassan ya farke wa Gombe kwallo daya a minti na 25.

Tun a ranar 16 ga watan Mayu Rangers ta hada maki 67 a saman teburi da ya ba ta zama gwarzuwar gasar bayan doke Bendel Insurance 2-0, sai dai kafin lashe gasar, Rangers ta ci wasanni 21 cikin 38 da ta buga, ta yi canjaras bakwai sannan ta yi rashin nasara sau 10.

Labarai Masu Nasaba

Ac Milan Na Tattaunawa Da Bayern Leverkusen Akan Yunkurin Daukar Boniface

Ronaldo Ya Samu Kyakkyawar Tarba A Hong Kong

Remo Stars ce ta kare a mataki na biyu da maki 65, sai kuma kungiyar Enyimba a mataki na uku da maki 63, wadanda suka samu gurbin shiga gasar zakarun Afirka ta badi.

Kamar yadda aka saba, kungiyoyi hudu na kasan teburi ne ke sauka daga babba zuwa karamar gasar ta firimiya wato Nijeriya National League (NNL). kungiyoyin su ne Sporting Lagos, Doma United, Heartland da kuma Gombe United.

Wasannin da aka buga a ranar Lahadi ne suka tabbatar da an kammala gasar kuma an buga jimillar wasanni 370, cikin kungiyoyi 20 da suka fafata tsawon kakar wasa daya kuma ita ce karo na 52 a tarihi.

 

Ga wasu abubuwa 10 da suka faru a gasar:

1. Dan wasan Enyimba, Bictor Mbaoma, shi ne kan gaba wajen jefa kwallaye a raga bayan ya ci kwallaye 16 a wasannin da ya fafata. 2. Dan wasan gaba na Kano Pillars, Yusuf Abdullahi, shi ne kadai ya ci kwallo sama da uku a wasa daya – inda ya ci Gombe United kwallo biyar a wasan da suka yi nasara 5-2 a kakar.

3 . ‘Yan wasa shida ne kacal suka ci kwallo uku rigis a wasa daya a kakar da aka kammala, su ne Robert Mizo (Bayelsa United), Yusuf Abdullahi (Kano Pillars) da dan wasa Albert Hillary (Plateau United), Nyima Nwagua (Ribers United), Silas Nenrot (Plateau United), Ubong Friday (Akwa United) da kuma Godwin Obaje (Plateau United).

4. Remo Stars ce ta fi kowacce kungiya karbar jan kati a kakar bana, inda aka bai wa ‘yan wasanta jan katin har sau bakwai – Enyimba ce ke biye mata da shida. 5 – Tun ana saura wasa daya a gama gasar Rangers ta dauki kofin wanda ba a fiya samun haka ba.

6. Doma United da ta sauka daga gasar, ta fi kowa buga wasa mai yawa ba tare da an zira mata kwallo a raga ba – da guda uku kawai ta dara zakarun gasar, wato kungiyar Rangers.

7 – Rangers sun fi kowa buga wasa mai yawa ba tare da rashin nasara ba, inda ta jera wasa 10 ba a doke ta ba – ta dara Doma United da wasa daya. 8 – Heartland wadda ta sauka daga gasar – ita ce ta fi kowa yawan wasa a jere ba tare da nasara ba. Ta buga wasa 11 babu nasara, sai kuma Doma da Gombe da suka buga 10-10 a jere babu nasara.

9 – Dan wasan Plateau United, Silas Nenrot, shi ne ya ci kwallo uku rigis a mafi kankantar lokaci a bana. Dan wasan gaban ya ci cikin minti 11 a wasan da suka doke Gombe United 4-0 a wasan mako 25.

10 – An ba da jan kati sau 49. 11 – An buga finareti 90, inda aka ci 70 kuma aka barar da 20.

12 – An ci kwallaye 848. 13 – Sau 29 kungiyoyoyi suka yi nasara a wasannin da suka buga a waje. 14 – Gombe ce ta fi kowa dibar kwallaye, inda aka zira mata 76 jimilla.

15 – An buga canjaras a wasa 86.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KofiRangers
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Amince Da Dokar Ba Da Agajin Gaggawa Da Aka Yi Wa Kwaskwarima

Next Post

Gaskiya Tsantsa Tinubu Ya Umarce Ni In Riƙa Faɗa – Ministan Yaɗa Labarai

Related

Boniface
Wasanni

Ac Milan Na Tattaunawa Da Bayern Leverkusen Akan Yunkurin Daukar Boniface

21 hours ago
Ronaldo Ya Samu Kyakkyawar Tarba A Hong Kong
Wasanni

Ronaldo Ya Samu Kyakkyawar Tarba A Hong Kong

2 days ago
Yadda Arsenal Ta Doke Manchester United Da Ci 1-0
Wasanni

Yadda Arsenal Ta Doke Manchester United Da Ci 1-0

4 days ago
Waye Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?
Wasanni

Waye Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?

4 days ago
Me Ya Sa Ciwon ACL Ya Zama Barazana Ga ‘Yan Wasan Kwallo?
Wasanni

Me Ya Sa Ciwon ACL Ya Zama Barazana Ga ‘Yan Wasan Kwallo?

4 days ago
An Biya Falcons Duk Kuɗin Alawus, Kyautar $100,000 Da Gidaje Ga Super Falcons
Wasanni

An Biya Falcons Duk Kuɗin Alawus, Kyautar $100,000 Da Gidaje Ga Super Falcons

6 days ago
Next Post
Gaskiya Tsantsa Tinubu Ya Umarce Ni In Riƙa Faɗa – Ministan Yaɗa Labarai

Gaskiya Tsantsa Tinubu Ya Umarce Ni In Riƙa Faɗa – Ministan Yaɗa Labarai

LABARAI MASU NASABA

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

August 21, 2025
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

August 21, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

August 21, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

August 21, 2025
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

August 21, 2025
Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

August 21, 2025
Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet

Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet

August 21, 2025
Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

August 21, 2025
Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

August 21, 2025
Boniface

Ac Milan Na Tattaunawa Da Bayern Leverkusen Akan Yunkurin Daukar Boniface

August 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.