• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Sabbin Gwamnoni 13 Suka Lafto Wa Jihohinsu Bashin Biliyan 226 Cikin Wata 6

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Gwamnoni

Akalla sabbin gwamnonin jihohin Nijeriya 13 ne suka karbi bashi biliyan 226.8 a cikin gida da waje cikin watanni shida kacal bayan sun hau karagar mulkin jihohinsu daban-daban, kamar yadda rahoton hukumar kula da basuka (DM0) ta fitar.

Rahoton hukumar DMO ya yi amfani da kididdigar basukan waje bisa la’akari da canjin dala kai naira 889.

  • Bayar Da Tallafin Wutar Lantarki Kaso 85 na Kara Nuna Tinubu Mai Kishin Jama’a Ne – Minista
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Gargadi Manoman Kan Sayar Da Kayan Aikin Da Ta Ba Su

Basukan wadanda suka hada da rancen cikin gida da masu ba da lamuni na kasa da kasa irinsu babban bankin duniya da kuma asusun bayar da lamuni ta duniya (IMF).

Rahoton hukumar DMO ta wallafa a shafinta zuwa ranar 20 ga watan Disamba 20 da 30 June 2023 ne aka kiyasce wannan adadin basukan.

Jerin jihohin da suka lafto wannan makudan kudaden a matsayin rance su ne, Jihar Benuwai, Kurus Ribas, Katsina, Neja, Filato, Ribas, Zamfara da kuma babban birnin tarayya wadanda suka samu biliyan 115.57 daga hannun masu ba da lamunin na cikin gida, yayin da gwamnonin Ebonyi, Kaduna, Kano, Neja, Filato, Sakwato, Taraba da Zamfara suka ciwo basukan dala miliyan 125.1, kimanin naira biliyan 111.24 daga masu ba da rance na waje.

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

Rahoton ya ci gaba da ba da bayani da cewa gwamnan Kurus Ribas, Bassey Out shi ne ya ciwo bashi mafi yawa a tsakanin wannan lokacin da ya kai naira biliyan 16.2, na bashin cikin gida da kuma dala miliyan 57.95 daga masu ba da lamuni na waje a tsakanin watan June zuwa Disamban 2023. Gwamnan Jihar Katsina ne ya biyo bayansa da ciwo bashin naira biliyan 36.93 da ya karu daga biliyan 62.37 zuwa biliyan 99.2 a watan Disamban 2023.

Jiha ta uku kuwa ita ce Jihar Neja da ta ciwo bashin cikin gida na naira biliyan 17.85 da ya karu daga biliyan 121.95 a June na 2023 zuwa biliyan 139.8 a watan Disamba.

Jihar Filato kuwa, bashin naira biliyan 16.32 ta ciwo, Ribas ta lafto wa kanta rancen naira biliyan 7.07, Zamfara kuwa naira biliyan 14.26 ta ciyo, yayin da birnin tarayya a karkashin jagorancin Nyesom Wike ta ciwo bashin naira biliyan 6.75 daga masu ba da lamuni na cikin gida.

A basukan waje kuwa, gwamna Jihar Ebnonyi, Francis Nwifuru ya amshi bashin dala miliyan 37.54, yayin da gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani ya karbi dala miliyan 17.69 daga masu ba da lamuni na waje.

Bugu da kari, gwamnonin Kano ya ci bashin dala miliyan 6.6, Neja dala miliyan 1.27, Filato dala 831,008, Sakkwato dala 499,472, Taraba dala miliyan 1.51, da kuma Zamfara mai bashin dala 655,563 daga masu ba da rance na waje.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
Manyan Labarai

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP
Labarai

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
Next Post
Sojoji Sun Kwato Makamai Da Babura, Sun Ceto Mutane 3 A Kaduna 

Sojoji Sun Hallaka 'Yan Bindiga 3 A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.