• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Tashar Jirgen Ruwan Apapa-Moniya Za Ta Taimaka Wa Masu Safarar Fitar Da Kaya

by Abubakar Abba
5 months ago
in Tattalin Arziki
0
Yadda Tashar Jirgen Ruwan Apapa-Moniya Za Ta Taimaka Wa Masu Safarar Fitar Da Kaya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yanzu, masu hada-hadar fitar da kaya da shigo da su a kasar nan, sun samu damar safarar kayansu a hanyar yin amfani da hanya a layin Jirgin kasa na Apapa-Moniya.

Wannan zai kara taimakawa wajen damar da damar fitar da kaya kai tsaye zuwa kasuwannin da ke a duniya.

  • Sin Ba Za Ta Razana Da Zuwan Yakin Cinikayya Ba
  • Trump Ya Dakatar da Harajin Da Sanya Wa Ƙasashen Duniya, Ya Ƙi Cire Wa China

A watan da ya gabata ne, aka kadamar da aikin ta hanyar yin hadaka da Hukumar Kula Da Sufurin Jiragen Kasa Ta Kasa, wanda a yanzu, ake gudanar da aiki sau uku a mako.

Jigilar kaya ta hanya, an jima a kasar tana zama babban kalubale, musamman wajen safarar kayan amfanin gona, musamman masu saurin lalacewa wanda hakan ke janyo yin asara da kuma haifar da jinjir da tsadar safarar kayan zuwa ga tashar Jiragen Ruwa.

Kazalika, kaddamar da wa za ta taimaka wajen saurin safarar amfanin gona da rage bata lokaci da kuma lalacewar kayan da aka yi safarsu.

Labarai Masu Nasaba

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

A makon da ya wuce ne, masu kula da wajen aijiye kaya a tashar Jiragen Ruwa ta Apapa, suka tattauna da masu safarar kayan amfanin gona da kuma wakilan Gwamnatin jihar Oyo domin tattaunawa kan yadda za a yi jigilar kayan amfanin gonar.

Manajan lura da sashen wajen ajiye kayan Steen Knudsen ne, ya jagoranci tawagar zuwa layin Dogon na Moniya, domin duba yadda aikin ke tafiya da ke a Ebute-Metta.

Knudsen ya bayyana cewa, aikin zai taimaka wajen ragewa masu jigilar kayan yin asara ta hanyar yin jigilarsu, ta hanya.

Ya kara da cewa, aikin zai kara taimakawa wajen jigilar kayan a cikin sauki.

Ita ma Jette Bjerrum, daga kasar Denmark ta bayyana cewa, kasar Denmark a shirye take wajen taimakawa Nijeriya don yin jigilar kayan amfanin gonar da kuma dabbobin da ake da bukatar yin jigilarsu, matukar Gwamnatin kasar ta amince da shirin na bunkasa hada-hadar kasuwancin.

Sai dai, masu ruwa da tsaki da sauran kwararru, sun nuna fargabar su, dabgane da batun tanadar tura kayan daga Ibadan ba tare da jigilarsu zuwa jihar Legas ba.

Shi kuwa mai bai wa gwamnatin jihar Oyo shawara ta musamman Tilewa Folami, aikin zai taimaka wajen kara bunkasa sadarwa a tsakanin babbar kasuwar da ke a Afrika ta tsakiya da kuma jihar ta Oyo.

Sauran masu ruwa da tsaki a fannin sun bayyana cewa, yin amfani da tashar ta Moniya, zai kara taimakawa wajen kai kayan a cikin sauki.

Shi kuwa Farfesa Frank Ojadi, wanda ya fito daga makarantar koyon kasuwanci da ke a jihar Legas ya sanar da cewa, aikin zai taimaka wajen rage jinkirin jigilar kaya a tashoshin Jiragen Ruwa na kasar.

A cewar Farfesa Frank Ojadi, fitacciyar Dalar Gyada ta da, wani alamu ne ragin da aka samu na sarrafa kaya, wanda hakan ya janyo saboda fuskatar karancin kayan aiki da kuma rashin watatattun layukan Dogo a kasar nan. “A wadancan shekarun baya, babu wadattun layukan Dogo a kasar nan, inda hakan ya sanya sai dai kawai a ajiye kayan, inda hakan ya sanya aka fara yin Dalar Gyada a kasar”. Inji Frank.

Frank ya yi gargadi da cewa, idan har Nijeriya kayan aikin da ake son yin amfani da su wajen jigilar kayan suka gaza, cimma burin da aka sanya a gaba, Nijeriya za ta ci gaba da fuskantar kalubalen safarar kaya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ApapaJiragen Ruwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Idris Ya Musanta Rahoton Wai Ya Ce A Yi Watsi Da Koken Gwamna Zulum Kan Rashin Tsaro A Borno

Next Post

Hanyoyi Biyar Na Kare Kajin Gidan Gona Daga Tsananin Zafi

Related

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Tattalin Arziki

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

4 days ago
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

2 weeks ago
tallafi
Tattalin Arziki

Kudaden Ajiya Na Asusun Nijeriya Ya Karu Zuwa Dala Biliyan 41

3 weeks ago
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

3 weeks ago
Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5
Tattalin Arziki

Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

3 weeks ago
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya
Tattalin Arziki

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

4 weeks ago
Next Post
Hanyoyi Biyar Na Kare Kajin Gidan Gona Daga Tsananin Zafi

Hanyoyi Biyar Na Kare Kajin Gidan Gona Daga Tsananin Zafi

LABARAI MASU NASABA

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.