• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Tashar Jirgen Ruwan Apapa-Moniya Za Ta Taimaka Wa Masu Safarar Fitar Da Kaya

by Abubakar Abba
3 months ago
in Tattalin Arziki
0
Yadda Tashar Jirgen Ruwan Apapa-Moniya Za Ta Taimaka Wa Masu Safarar Fitar Da Kaya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yanzu, masu hada-hadar fitar da kaya da shigo da su a kasar nan, sun samu damar safarar kayansu a hanyar yin amfani da hanya a layin Jirgin kasa na Apapa-Moniya.

Wannan zai kara taimakawa wajen damar da damar fitar da kaya kai tsaye zuwa kasuwannin da ke a duniya.

  • Sin Ba Za Ta Razana Da Zuwan Yakin Cinikayya Ba
  • Trump Ya Dakatar da Harajin Da Sanya Wa Ƙasashen Duniya, Ya Ƙi Cire Wa China

A watan da ya gabata ne, aka kadamar da aikin ta hanyar yin hadaka da Hukumar Kula Da Sufurin Jiragen Kasa Ta Kasa, wanda a yanzu, ake gudanar da aiki sau uku a mako.

Jigilar kaya ta hanya, an jima a kasar tana zama babban kalubale, musamman wajen safarar kayan amfanin gona, musamman masu saurin lalacewa wanda hakan ke janyo yin asara da kuma haifar da jinjir da tsadar safarar kayan zuwa ga tashar Jiragen Ruwa.

Kazalika, kaddamar da wa za ta taimaka wajen saurin safarar amfanin gona da rage bata lokaci da kuma lalacewar kayan da aka yi safarsu.

Labarai Masu Nasaba

Kungiyar MEMAN Ta Yi Maraba Da Shirin Dangote Na Rabar Da Man Fetur

NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku

A makon da ya wuce ne, masu kula da wajen aijiye kaya a tashar Jiragen Ruwa ta Apapa, suka tattauna da masu safarar kayan amfanin gona da kuma wakilan Gwamnatin jihar Oyo domin tattaunawa kan yadda za a yi jigilar kayan amfanin gonar.

Manajan lura da sashen wajen ajiye kayan Steen Knudsen ne, ya jagoranci tawagar zuwa layin Dogon na Moniya, domin duba yadda aikin ke tafiya da ke a Ebute-Metta.

Knudsen ya bayyana cewa, aikin zai taimaka wajen ragewa masu jigilar kayan yin asara ta hanyar yin jigilarsu, ta hanya.

Ya kara da cewa, aikin zai kara taimakawa wajen jigilar kayan a cikin sauki.

Ita ma Jette Bjerrum, daga kasar Denmark ta bayyana cewa, kasar Denmark a shirye take wajen taimakawa Nijeriya don yin jigilar kayan amfanin gonar da kuma dabbobin da ake da bukatar yin jigilarsu, matukar Gwamnatin kasar ta amince da shirin na bunkasa hada-hadar kasuwancin.

Sai dai, masu ruwa da tsaki da sauran kwararru, sun nuna fargabar su, dabgane da batun tanadar tura kayan daga Ibadan ba tare da jigilarsu zuwa jihar Legas ba.

Shi kuwa mai bai wa gwamnatin jihar Oyo shawara ta musamman Tilewa Folami, aikin zai taimaka wajen kara bunkasa sadarwa a tsakanin babbar kasuwar da ke a Afrika ta tsakiya da kuma jihar ta Oyo.

Sauran masu ruwa da tsaki a fannin sun bayyana cewa, yin amfani da tashar ta Moniya, zai kara taimakawa wajen kai kayan a cikin sauki.

Shi kuwa Farfesa Frank Ojadi, wanda ya fito daga makarantar koyon kasuwanci da ke a jihar Legas ya sanar da cewa, aikin zai taimaka wajen rage jinkirin jigilar kaya a tashoshin Jiragen Ruwa na kasar.

A cewar Farfesa Frank Ojadi, fitacciyar Dalar Gyada ta da, wani alamu ne ragin da aka samu na sarrafa kaya, wanda hakan ya janyo saboda fuskatar karancin kayan aiki da kuma rashin watatattun layukan Dogo a kasar nan. “A wadancan shekarun baya, babu wadattun layukan Dogo a kasar nan, inda hakan ya sanya sai dai kawai a ajiye kayan, inda hakan ya sanya aka fara yin Dalar Gyada a kasar”. Inji Frank.

Frank ya yi gargadi da cewa, idan har Nijeriya kayan aikin da ake son yin amfani da su wajen jigilar kayan suka gaza, cimma burin da aka sanya a gaba, Nijeriya za ta ci gaba da fuskantar kalubalen safarar kaya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ApapaJiragen Ruwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Idris Ya Musanta Rahoton Wai Ya Ce A Yi Watsi Da Koken Gwamna Zulum Kan Rashin Tsaro A Borno

Next Post

Hanyoyi Biyar Na Kare Kajin Gidan Gona Daga Tsananin Zafi

Related

Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Kungiyar MEMAN Ta Yi Maraba Da Shirin Dangote Na Rabar Da Man Fetur

51 minutes ago
NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku
Tattalin Arziki

NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku

2 hours ago
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

6 days ago
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

4 weeks ago
Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

1 month ago
Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

1 month ago
Next Post
Hanyoyi Biyar Na Kare Kajin Gidan Gona Daga Tsananin Zafi

Hanyoyi Biyar Na Kare Kajin Gidan Gona Daga Tsananin Zafi

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

July 4, 2025
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Kungiyar MEMAN Ta Yi Maraba Da Shirin Dangote Na Rabar Da Man Fetur

July 4, 2025
NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku

NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku

July 4, 2025
Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

July 3, 2025
Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

July 3, 2025
Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

July 3, 2025
Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

July 3, 2025
Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

July 3, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

July 3, 2025
Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

July 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.