ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Tashar Jirgen Ruwan Apapa-Moniya Za Ta Taimaka Wa Masu Safarar Fitar Da Kaya

by Abubakar Abba
1 year ago
Apapa

A yanzu, masu hada-hadar fitar da kaya da shigo da su a kasar nan, sun samu damar safarar kayansu a hanyar yin amfani da hanya a layin Jirgin kasa na Apapa-Moniya.

Wannan zai kara taimakawa wajen damar da damar fitar da kaya kai tsaye zuwa kasuwannin da ke a duniya.

  • Sin Ba Za Ta Razana Da Zuwan Yakin Cinikayya Ba
  • Trump Ya Dakatar da Harajin Da Sanya Wa Ƙasashen Duniya, Ya Ƙi Cire Wa China

A watan da ya gabata ne, aka kadamar da aikin ta hanyar yin hadaka da Hukumar Kula Da Sufurin Jiragen Kasa Ta Kasa, wanda a yanzu, ake gudanar da aiki sau uku a mako.

ADVERTISEMENT

Jigilar kaya ta hanya, an jima a kasar tana zama babban kalubale, musamman wajen safarar kayan amfanin gona, musamman masu saurin lalacewa wanda hakan ke janyo yin asara da kuma haifar da jinjir da tsadar safarar kayan zuwa ga tashar Jiragen Ruwa.

Kazalika, kaddamar da wa za ta taimaka wajen saurin safarar amfanin gona da rage bata lokaci da kuma lalacewar kayan da aka yi safarsu.

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

A makon da ya wuce ne, masu kula da wajen aijiye kaya a tashar Jiragen Ruwa ta Apapa, suka tattauna da masu safarar kayan amfanin gona da kuma wakilan Gwamnatin jihar Oyo domin tattaunawa kan yadda za a yi jigilar kayan amfanin gonar.

Manajan lura da sashen wajen ajiye kayan Steen Knudsen ne, ya jagoranci tawagar zuwa layin Dogon na Moniya, domin duba yadda aikin ke tafiya da ke a Ebute-Metta.

Knudsen ya bayyana cewa, aikin zai taimaka wajen ragewa masu jigilar kayan yin asara ta hanyar yin jigilarsu, ta hanya.

Ya kara da cewa, aikin zai kara taimakawa wajen jigilar kayan a cikin sauki.

Ita ma Jette Bjerrum, daga kasar Denmark ta bayyana cewa, kasar Denmark a shirye take wajen taimakawa Nijeriya don yin jigilar kayan amfanin gonar da kuma dabbobin da ake da bukatar yin jigilarsu, matukar Gwamnatin kasar ta amince da shirin na bunkasa hada-hadar kasuwancin.

Sai dai, masu ruwa da tsaki da sauran kwararru, sun nuna fargabar su, dabgane da batun tanadar tura kayan daga Ibadan ba tare da jigilarsu zuwa jihar Legas ba.

Shi kuwa mai bai wa gwamnatin jihar Oyo shawara ta musamman Tilewa Folami, aikin zai taimaka wajen kara bunkasa sadarwa a tsakanin babbar kasuwar da ke a Afrika ta tsakiya da kuma jihar ta Oyo.

Sauran masu ruwa da tsaki a fannin sun bayyana cewa, yin amfani da tashar ta Moniya, zai kara taimakawa wajen kai kayan a cikin sauki.

Shi kuwa Farfesa Frank Ojadi, wanda ya fito daga makarantar koyon kasuwanci da ke a jihar Legas ya sanar da cewa, aikin zai taimaka wajen rage jinkirin jigilar kaya a tashoshin Jiragen Ruwa na kasar.

A cewar Farfesa Frank Ojadi, fitacciyar Dalar Gyada ta da, wani alamu ne ragin da aka samu na sarrafa kaya, wanda hakan ya janyo saboda fuskatar karancin kayan aiki da kuma rashin watatattun layukan Dogo a kasar nan. “A wadancan shekarun baya, babu wadattun layukan Dogo a kasar nan, inda hakan ya sanya sai dai kawai a ajiye kayan, inda hakan ya sanya aka fara yin Dalar Gyada a kasar”. Inji Frank.

Frank ya yi gargadi da cewa, idan har Nijeriya kayan aikin da ake son yin amfani da su wajen jigilar kayan suka gaza, cimma burin da aka sanya a gaba, Nijeriya za ta ci gaba da fuskantar kalubalen safarar kaya.

Apapa
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Tattalin Arziki

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Next Post
Hanyoyi Biyar Na Kare Kajin Gidan Gona Daga Tsananin Zafi

Hanyoyi Biyar Na Kare Kajin Gidan Gona Daga Tsananin Zafi

LABARAI MASU NASABA

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

June 22, 2026

Mutane 842 Ne Suka Rasa Ransu, Aka Yi Garkuwa Da Sama Da 270 A Watan Mayu – Rahoto

June 21, 2026
PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar  Jamiyyar

PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar Jamiyyar

June 21, 2026
An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

June 21, 2026
An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 21, 2026
Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

June 21, 2026
Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 21, 2026
Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

June 21, 2026
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

June 21, 2026
Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.