ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Tashar Jirgen Ruwan Apapa-Moniya Za Ta Taimaka Wa Masu Safarar Fitar Da Kaya

by Abubakar Abba
1 year ago
Apapa

A yanzu, masu hada-hadar fitar da kaya da shigo da su a kasar nan, sun samu damar safarar kayansu a hanyar yin amfani da hanya a layin Jirgin kasa na Apapa-Moniya.

Wannan zai kara taimakawa wajen damar da damar fitar da kaya kai tsaye zuwa kasuwannin da ke a duniya.

  • Sin Ba Za Ta Razana Da Zuwan Yakin Cinikayya Ba
  • Trump Ya Dakatar da Harajin Da Sanya Wa Ƙasashen Duniya, Ya Ƙi Cire Wa China

A watan da ya gabata ne, aka kadamar da aikin ta hanyar yin hadaka da Hukumar Kula Da Sufurin Jiragen Kasa Ta Kasa, wanda a yanzu, ake gudanar da aiki sau uku a mako.

ADVERTISEMENT

Jigilar kaya ta hanya, an jima a kasar tana zama babban kalubale, musamman wajen safarar kayan amfanin gona, musamman masu saurin lalacewa wanda hakan ke janyo yin asara da kuma haifar da jinjir da tsadar safarar kayan zuwa ga tashar Jiragen Ruwa.

Kazalika, kaddamar da wa za ta taimaka wajen saurin safarar amfanin gona da rage bata lokaci da kuma lalacewar kayan da aka yi safarsu.

LABARAI MASU NASABA

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

A makon da ya wuce ne, masu kula da wajen aijiye kaya a tashar Jiragen Ruwa ta Apapa, suka tattauna da masu safarar kayan amfanin gona da kuma wakilan Gwamnatin jihar Oyo domin tattaunawa kan yadda za a yi jigilar kayan amfanin gonar.

Manajan lura da sashen wajen ajiye kayan Steen Knudsen ne, ya jagoranci tawagar zuwa layin Dogon na Moniya, domin duba yadda aikin ke tafiya da ke a Ebute-Metta.

Knudsen ya bayyana cewa, aikin zai taimaka wajen ragewa masu jigilar kayan yin asara ta hanyar yin jigilarsu, ta hanya.

Ya kara da cewa, aikin zai kara taimakawa wajen jigilar kayan a cikin sauki.

Ita ma Jette Bjerrum, daga kasar Denmark ta bayyana cewa, kasar Denmark a shirye take wajen taimakawa Nijeriya don yin jigilar kayan amfanin gonar da kuma dabbobin da ake da bukatar yin jigilarsu, matukar Gwamnatin kasar ta amince da shirin na bunkasa hada-hadar kasuwancin.

Sai dai, masu ruwa da tsaki da sauran kwararru, sun nuna fargabar su, dabgane da batun tanadar tura kayan daga Ibadan ba tare da jigilarsu zuwa jihar Legas ba.

Shi kuwa mai bai wa gwamnatin jihar Oyo shawara ta musamman Tilewa Folami, aikin zai taimaka wajen kara bunkasa sadarwa a tsakanin babbar kasuwar da ke a Afrika ta tsakiya da kuma jihar ta Oyo.

Sauran masu ruwa da tsaki a fannin sun bayyana cewa, yin amfani da tashar ta Moniya, zai kara taimakawa wajen kai kayan a cikin sauki.

Shi kuwa Farfesa Frank Ojadi, wanda ya fito daga makarantar koyon kasuwanci da ke a jihar Legas ya sanar da cewa, aikin zai taimaka wajen rage jinkirin jigilar kaya a tashoshin Jiragen Ruwa na kasar.

A cewar Farfesa Frank Ojadi, fitacciyar Dalar Gyada ta da, wani alamu ne ragin da aka samu na sarrafa kaya, wanda hakan ya janyo saboda fuskatar karancin kayan aiki da kuma rashin watatattun layukan Dogo a kasar nan. “A wadancan shekarun baya, babu wadattun layukan Dogo a kasar nan, inda hakan ya sanya sai dai kawai a ajiye kayan, inda hakan ya sanya aka fara yin Dalar Gyada a kasar”. Inji Frank.

Frank ya yi gargadi da cewa, idan har Nijeriya kayan aikin da ake son yin amfani da su wajen jigilar kayan suka gaza, cimma burin da aka sanya a gaba, Nijeriya za ta ci gaba da fuskantar kalubalen safarar kaya.

Apapa
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tattalin Arziki

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

July 11, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Tattalin Arziki

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani
Tattalin Arziki

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
Next Post
Hanyoyi Biyar Na Kare Kajin Gidan Gona Daga Tsananin Zafi

Hanyoyi Biyar Na Kare Kajin Gidan Gona Daga Tsananin Zafi

LABARAI MASU NASABA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

July 12, 2026
NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

July 12, 2026
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

July 12, 2026
NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

July 12, 2026
inec

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina

July 12, 2026
Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

July 11, 2026
Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

July 11, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

July 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.