ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, September 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hanyoyi Biyar Na Kare Kajin Gidan Gona Daga Tsananin Zafi

by Abubakar Abba
1 year ago
Kaji

Hukumar Kula da Yanayi ta Kasa wato (NIMET), ta yi hasashen cewa; za a fuskanci tsananin zafin rana a shekarar 2025 a fadin Nijeriya, musamman a lokutan dare da kuma rana, inda kuma rana za ta yi dumi a watannin Janairu, Maris da kuma Mayu.

Haka zalika, Hukumar Kula da Yanayi ta Duniya (WMO) ta sanar da cewa, a shekarar 2024 ne, aka fi fuskantar tsananin zafin rana a cikin shekaru 175 da suka gabata.

  • Yadda Tashar Jirgen Ruwan Apapa-Moniya Za Ta Taimaka Wa Masu Safarar Fitar Da Kaya
  • NIMASA Za Ta Adana Wa Nijeriya Dala Biliyan 400 A Shekara Daga Cazar Kudaden Safarar Kaya

Kazalika, hukumar ta WMO ta yi gargadin cewa, shekarar 2025 za ta kasance mafi tsananin zafin rana.

ADVERTISEMENT

Wannan karuwar tsananin zafin ranar, ba wai kawai za ta shafi amfanin gona ba ne, za kuma ta zama kalubale ga lafiyar kajin gidan gona.

Misali, kajin gidan gona masu saurin girma kamar samfurin da ake kira a turance da ‘Broilers’, na da gajeren lokacin jurewa zafin rana, musamman duba da cewa; ba sa iya jurewa tsananin zafin ranar.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Hanyoyi Biyar Da Mai Kiwon Kajin Gidan Gona Zai Kare Kajinsa Daga Tsananin Zafin Rana.

1- A Tabbatar An Sama Musu Wadacciyar Iska A Dakin Kwanansu:

Ana bukatar mai kiwon kajin ya tabbatar ya sama musu wadatacciyar iska a dakin kwanansu, ana kuma bukatar a yi wa shigifar dakinsu fenti yadda za ta rika rage zafin ranar da kuma samar da kayan koyon da za su sanyaya dakin kwanansu.

Haka kuma, ana bukatar a rika sanya musu na’urar da ke sanyaya daki, wadanda za su rika rage zafin ranar, akalla na’urar ta kasance mai ma’unin yanayi daga 5 zuwa 10°C.

2- Sanya Na’urar Sanya Daki:

Domin samun saukin yanayin zafin rana, ana bukatar mai kiwo ya sanya musu na’ura a dakin kwanansu, domin rika sanyaya dakin, yadda jikinsu zai rika yin sanyi.

Ana kuma bukatar masu kiwon, su rika sanya musu Fanka a dakin kwanansu, wanda hakan zai ba su damar samun wadatacciyar iska.

3- Shayar Da Su Wadataccen Ruwan Sha:

Tanadar musu da wadataccen ruwan sha, na taimaka musu wajen samun sinadaran da za su kara inganta rayuwarsu da kuma jurewa tsananin zafin rana.

Kazalika, ana bukatar masu kiwon su rika zuba musu garin sinadarin ‘glucose da amino acids’, domin kara musu karsashi da kuma kara karfafa garkuwar jikinsu.

4- Sama Musu Da Sauyin Ciyar Da Su Abinci:

Ana bukatar masu kiwonsu, su rika ciyar da su abinci mai dauke da sinadari kamar na ‘Bitamin E da selenium’, wadanda za su taimaka wa lafiyarsu.

Wadannan sinadarai, na matukar bayar da gudunmawa wajen ba su kariya daga jin tsananin zafin rana.

5- Sanya Ido Kan Yiwuwar Barkewar Wata Cuta:

Ana bukatar mai kiwon kajin ya tabbatar yana yawan sanya ido kan kajin, domin gano wasu alamomin da za su iya sanya su ji tsananin zafin rana ko kuma kamuwa da wasu kwayoyin cuta, musamman domin daukar matakan gaggawa na kare lafiyarsu.

Ana kuma bukatar mai kiwonsu ya tabbatar yana ciyar da su abinci mai gina jiki, wanda hakan zai taimaka musu daga saurin kamuwa da kwayoyin cututtuka.

Kaji
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Tinubu Ya Umarci Ma’aikatu Su Sayi Motoci Masu Amfani Da Gas

Dalilin Nijeriya Na Karbo Bashin Dala Biliyan 12 Daga Kasar Japan

LABARAI MASU NASABA

NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Mene Ne Ra’ayinku Kan Dawo Da Tallafin Man Fetur Ko Barin Sa?

September 12, 2026
Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

September 11, 2026
Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

September 11, 2026
Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

September 11, 2026
Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

September 11, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

Dalilan Da Ya Sa Jam’iyyun Siyasa Suka Jinkirta Ƙaddamar Da Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen

September 11, 2026
Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

September 11, 2026
Za A Ci ’Yan Siyasa Masu Kalaman Ɓatanci Tarar Miliyan 10 Da Ɗaurin Watanni 12 — INEC

2027: A Karon Farko INEC Za Ta Ƙaddamar Da Na’urar Bibiyar Zaɓen Nijeriya

September 11, 2026
Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

September 11, 2026
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026  Mrs Zubaida Umar

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026 Mrs Zubaida Umar

September 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.