• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa

by Leadership Hausa
3 years ago
in Rahotonni
0
Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Edita, don Allah ka ba ni fili a wannan jarida tamu mai farin jini don in kara sautin amon murya ta kan sauran muryoyin da ke ta kiraye-kiraye ga gwamnatin tarayya da kungiyar ASUU game da yajin aikin da kungiyar ke yi tsawon kimanin watanni takwas kenan.

Yau kusan wata 8 kenan jami’oi a Nijeriya suke a kulle sakamakon rikicin da yaki ci yaki cinyewa tsakanin Gwamnati da ASUU, rikicin da ya sam oasali tun kusan 1999, an yi gwamnatoci da dama wadanda suke gadar wannan rikici kuma haka suke shudewa ba tare da kawo karshen shi ba, a namu bangarenmu dalibai wannan rikicin ba karamin cutar da rayuwarmu yake ba, domin duk lokacin da aka tafi irin wannan yajin aiki, komai na karatunmu tsayawa yake, kuma sannan da yawan mu komawa gida mukeyi muna zaman banza zaman jiran tsammani, saboda ko da mutum ya nemi wani abin yi dole sai dai ya zama na wucin gadi.

Tun daga lokacin da aka fara rikita rikita tsakanin gwamnatin tarayya da ASUU ba a taba yin gwamnati da dalibai muka sanya rai da tsammanin za ta kawo karshen wannan rikici ba, irin wannan gwamnati ta mai girma shugaban kasa Muhammad Buhari, hakan kuwa ya samo asali ne sakamakon irin kyautata mata zato da muke yi da kuma yadda muka ga tana yawan ambatawa a wajen yakin neman zabe cewa zata kula da rayuwar matasa, kuma zata bai wa harkar ilimi mahimmanci, amma sai dai kash gashi gwamnati tana shirin karewa lamarina kokarin chanjawa, a ranar 26 ga watan June, 2022 mun hango minister ma’aikata a fadar gwamanati da keAbuja, bayan kammala zaman Majalisar Ministoci watau FEC yana mana Albishir da cewa kusan komai ya zo karshe yanzu jira kawai suke yi hukumomin da abin ya shafa su tattara reports zuwa ranar laraba sai a yi sign, jin wannan labarin ya faranta mana rai sosai, ammah sai gashi mun ji shiru har zuwa yanzu.

Wani abu da ya kara daga mana hankali sai ji muka yi a ranar Litinin 4 ga watan Yuli Shugaban Kungiyar ASUU yana wata magana mai kama da habaici, inda ya cewa “a shirye suke su jira gwamnati ta neme su ko da nan da shekara 2 ne, inda ya kara da cewa su da membobinsu zasu tuka mortar hanya, su siyar da gyada domin su samu abin da zasu ci ”Wannann maganar ta daga mana hankali gaskiya, domin duk dalibi na kwarai dole ya tausayawa malamansa tsawon wata 8 basu da Albashi, da wannan muke rokon gwamnatin tarayyah karkashin shugabancin Muhammadu Buhari, don Allah su tausayawa mana, su cika mana Alkawarin da Suka mana lokacin Campaign, Su tausayawa halin da yan uwanmu matasa ka iya fadawa sakamakon wannan dogon yajin Aiki.

Umar Kabir Dakata, marubuci ne kuma matashi mai sharhi kan harkokin ilimi da rayuwar matasa, shi ne kuma shugaban kungiyar Arewa Media Writers na Jihar Kano.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DalibaigwamnatiMalamaiRa'ayiYajin Aikin ASUU
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Tana Sa Lura Ga Yanayin Da Ake Ciki A Burkina Faso

Next Post

Manchester United Ta Kafa Mummunan Tarihi A Watannin Oktoba

Related

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

4 weeks ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

1 month ago
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Rahotonni

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

1 month ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Rahotonni

Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto

1 month ago
Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi
Rahotonni

Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi

1 month ago
Tinubu
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

2 months ago
Next Post
Manchester United Ta Kafa Mummunan Tarihi A Watannin Oktoba

Manchester United Ta Kafa Mummunan Tarihi A Watannin Oktoba

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.