• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaki Da Safarar Mutane A Duniya

by Leadership Hausa
3 years ago
in Rahotonni
0
Yaki Da Safarar Mutane A Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Al’ummar Duniya ta ware ranar 30 ga watan Yuli na kowacce shekara don fadakar tare da tunatar da al’umma illar safarar mutane a duniya. 

Wannan abin kyamar ya samo asali ne ga yadda aka tsani yadda ake gudanar da safarar mutane a matsayin bayi a shekarun baya kuma, duniya ta dauki matakin watsi da wannan sana’ar musamman ganin yadda ake cin zarafin mutanen da aka yi safararsu tare da kuma ci da guminsu.

  • Wang Wenbin: Hannuwan ‘Yan Siyasar Amurka Da “‘Yan Ina Da Yaki” Na Jike Da Jinin Al’ummun Gabas Ta Tsakiya
  • Yadda Rijiya Ta Rufta Da Uba Da Ɗansa A Kano

Taken bikin na wannan shekarar shi ne yadda ake amfani da kafafen sadarwa na zamani wajen amfani da su don safarar mutane a sassan duniya da nemo hanyoyin dakile harkokin masu safarar mutane.

Majalisar dinkin Duniya ta bayar da shawarar daukar matakin fadakar da jama’a bukatar taka-tsantsan wajen amfani da kafafen sadarwa na zamani don kaucewa fadawa tarkon masu safarar mutane wadanda suke amfani da jahilcin mutane wajen cutar da su.

Ana sa ran amfani da taken na wannan shekarar don fito da dukkan hanyoyin da masu safarar mutane za su iya amfani da su wajen aiwatar da mugun aikin nasu tare da fadakar da al’umma hanyoyin kauce wa fadawa tarkon nasu.

Labarai Masu Nasaba

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

“Masu safarar mutane na amfani da kafafen sadarwa wajen yaudarar mutane ciki har da yara kanana, suna amfani da hanyoyi dabandaban don jawo hankalin mutane, kamar yadda Majalisar dinkin duniya ta ankarar.

“Haka kuma masu safarar mutane na amfani da sirrikan kafafen sadarwa wajen hulda a tsakanisu ba tare da al’umma sun fahimci abin da ake ciki ba suna kuma ankarar da junansu don kaucewa fadawa hannun jami’an tsaro.”

A jawabinsa na wannan ranar, Shugaban Majalisar dinkin Duniya, Antonio Guetteres, ya bayyana cewa, wadanda suka fi fadawa komar masu safarar mutane sun hada da mata da yara kanana.

“Masu safarar mutane na amfani da rauninsu ta hanyar amfani da kafofin sadarwa na zamani tare da kwarewarsu na kimiyya da fasaha wajen bibiya tare da yaudarar mutane, sukan kuma kwadaitar da su samun ayyuka a kasashen waje.”

Hukumar majalisar dinkin mai kula da masu aikata manyan laifufkka (UNODC) a rahotonta na shekarar 2018, ta bayyana cewa an samu nasarar gano akalla wadanda aka yi safarar su har mutum 50,000 da aka bayar da rahoton su a kasashe 148.

Haka kuma an fahimci cewa, kashi 50 na wadanda aka yi safarar na su ana yi ne don sanya su a sana’ar karuwanci a kasashen duniya, kashi 38 kuma ana jefa su ayyukan karfi ne ba tare da albashi ba.

An kuma gano cewa, kashi 46 daga cikin wadanda aka yi safarar nasu mata ne yayin da kuma kashi 19 kananan yara mata ne.

Daya daga cikin mutum uku daga wadanda aka yi safarar su suna kasancewa yara ne kanana yayin da kuma yawan yaran da ake safarar yana karuwa a kullum haka kuma yawan yara maza da aka yi safara su a cikin shekara 15 ya karu da kashi 5 a fadin duniya a ‘yan shekarun nan.

Majalisar ta kuma sanar da cewa, rahotanni ya nuna cewa, kashi 79 na wadanda ake safarar ana yin hakan ne don jefa su ayyukan karuwanci.

An kuma fi farauto ‘yan mata don amfani da su wanannan sana’ar. A rahotonta na shekarar 2021, hukumar yaki da safarar mutane a Nijeriya (NAPTIP), ta bayyana cewa, an samu rahoton safarar mtane har 1,112 yayin da kuma kashi 35.8 a cikin su an farauto su ne don abin da ya shafi harkar karuwanci da zama bakin haure.

Haka kuma rahoton UNDC na shekarar 2020 ya nuna cewa, kashi 60 na wadanda aka yi safarar su yankin Afrika Yamma yara ne kanana, an kuma karfafa matakai don kawo karshen wananan lamarin da gaggawa.

Yawancin masu safarar na fakewa ne da halin talauci da al’umma ke ciki ne wajen yaudarar mutane wadanda suke fafutukar tserewa daga kangin talaucin da suke fuskantar da kuma barazana na rayuwa a fannoni da dama kamar yadda kungiyar Lauyoyi Mata ta duniya (FIDA) ta bayyana a taron kwanakin baya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BincikeLeadership HausaManyan LabaraiRa'ayiRahoto
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wang Wenbin: Hannuwan ‘Yan Siyasar Amurka Da “‘Yan Ina Da Yaki” Na Jike Da Jinin Al’ummun Gabas Ta Tsakiya

Next Post

Tsadar Farashi: Yadda ‘Yan Nijeriya Suka Koma Sayen Kaya Masu Araha

Related

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

18 hours ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

7 days ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

7 days ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

2 weeks ago
Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

2 months ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

2 months ago
Next Post
Tsadar Farashi: Yadda ‘Yan Nijeriya Suka Koma Sayen Kaya Masu Araha

Tsadar Farashi: Yadda 'Yan Nijeriya Suka Koma Sayen Kaya Masu Araha

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.