ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaki Da Safarar Mutane A Duniya

by Leadership Hausa
3 years ago
Safara

Al’ummar Duniya ta ware ranar 30 ga watan Yuli na kowacce shekara don fadakar tare da tunatar da al’umma illar safarar mutane a duniya. 

Wannan abin kyamar ya samo asali ne ga yadda aka tsani yadda ake gudanar da safarar mutane a matsayin bayi a shekarun baya kuma, duniya ta dauki matakin watsi da wannan sana’ar musamman ganin yadda ake cin zarafin mutanen da aka yi safararsu tare da kuma ci da guminsu.

  • Wang Wenbin: Hannuwan ‘Yan Siyasar Amurka Da “‘Yan Ina Da Yaki” Na Jike Da Jinin Al’ummun Gabas Ta Tsakiya
  • Yadda Rijiya Ta Rufta Da Uba Da Ɗansa A Kano

Taken bikin na wannan shekarar shi ne yadda ake amfani da kafafen sadarwa na zamani wajen amfani da su don safarar mutane a sassan duniya da nemo hanyoyin dakile harkokin masu safarar mutane.

ADVERTISEMENT

Majalisar dinkin Duniya ta bayar da shawarar daukar matakin fadakar da jama’a bukatar taka-tsantsan wajen amfani da kafafen sadarwa na zamani don kaucewa fadawa tarkon masu safarar mutane wadanda suke amfani da jahilcin mutane wajen cutar da su.

Ana sa ran amfani da taken na wannan shekarar don fito da dukkan hanyoyin da masu safarar mutane za su iya amfani da su wajen aiwatar da mugun aikin nasu tare da fadakar da al’umma hanyoyin kauce wa fadawa tarkon nasu.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

“Masu safarar mutane na amfani da kafafen sadarwa wajen yaudarar mutane ciki har da yara kanana, suna amfani da hanyoyi dabandaban don jawo hankalin mutane, kamar yadda Majalisar dinkin duniya ta ankarar.

“Haka kuma masu safarar mutane na amfani da sirrikan kafafen sadarwa wajen hulda a tsakanisu ba tare da al’umma sun fahimci abin da ake ciki ba suna kuma ankarar da junansu don kaucewa fadawa hannun jami’an tsaro.”

A jawabinsa na wannan ranar, Shugaban Majalisar dinkin Duniya, Antonio Guetteres, ya bayyana cewa, wadanda suka fi fadawa komar masu safarar mutane sun hada da mata da yara kanana.

“Masu safarar mutane na amfani da rauninsu ta hanyar amfani da kafofin sadarwa na zamani tare da kwarewarsu na kimiyya da fasaha wajen bibiya tare da yaudarar mutane, sukan kuma kwadaitar da su samun ayyuka a kasashen waje.”

Hukumar majalisar dinkin mai kula da masu aikata manyan laifufkka (UNODC) a rahotonta na shekarar 2018, ta bayyana cewa an samu nasarar gano akalla wadanda aka yi safarar su har mutum 50,000 da aka bayar da rahoton su a kasashe 148.

Haka kuma an fahimci cewa, kashi 50 na wadanda aka yi safarar na su ana yi ne don sanya su a sana’ar karuwanci a kasashen duniya, kashi 38 kuma ana jefa su ayyukan karfi ne ba tare da albashi ba.

An kuma gano cewa, kashi 46 daga cikin wadanda aka yi safarar nasu mata ne yayin da kuma kashi 19 kananan yara mata ne.

Daya daga cikin mutum uku daga wadanda aka yi safarar su suna kasancewa yara ne kanana yayin da kuma yawan yaran da ake safarar yana karuwa a kullum haka kuma yawan yara maza da aka yi safara su a cikin shekara 15 ya karu da kashi 5 a fadin duniya a ‘yan shekarun nan.

Majalisar ta kuma sanar da cewa, rahotanni ya nuna cewa, kashi 79 na wadanda ake safarar ana yin hakan ne don jefa su ayyukan karuwanci.

An kuma fi farauto ‘yan mata don amfani da su wanannan sana’ar. A rahotonta na shekarar 2021, hukumar yaki da safarar mutane a Nijeriya (NAPTIP), ta bayyana cewa, an samu rahoton safarar mtane har 1,112 yayin da kuma kashi 35.8 a cikin su an farauto su ne don abin da ya shafi harkar karuwanci da zama bakin haure.

Haka kuma rahoton UNDC na shekarar 2020 ya nuna cewa, kashi 60 na wadanda aka yi safarar su yankin Afrika Yamma yara ne kanana, an kuma karfafa matakai don kawo karshen wananan lamarin da gaggawa.

Yawancin masu safarar na fakewa ne da halin talauci da al’umma ke ciki ne wajen yaudarar mutane wadanda suke fafutukar tserewa daga kangin talaucin da suke fuskantar da kuma barazana na rayuwa a fannoni da dama kamar yadda kungiyar Lauyoyi Mata ta duniya (FIDA) ta bayyana a taron kwanakin baya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba
Manyan Labarai

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

November 12, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
Next Post
Tsadar Farashi: Yadda ‘Yan Nijeriya Suka Koma Sayen Kaya Masu Araha

Tsadar Farashi: Yadda 'Yan Nijeriya Suka Koma Sayen Kaya Masu Araha

LABARAI MASU NASABA

Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

November 13, 2025
Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

November 13, 2025
Nijeriya Za Ta Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Gusau

Nijeriya Za Ta Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Gusau

November 13, 2025
‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

November 13, 2025
Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

November 13, 2025
Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025
Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

November 13, 2025
Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.