• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaki Da Safarar Mutane A Duniya

by Leadership Hausa
3 years ago
in Rahotonni
0
Yaki Da Safarar Mutane A Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Al’ummar Duniya ta ware ranar 30 ga watan Yuli na kowacce shekara don fadakar tare da tunatar da al’umma illar safarar mutane a duniya. 

Wannan abin kyamar ya samo asali ne ga yadda aka tsani yadda ake gudanar da safarar mutane a matsayin bayi a shekarun baya kuma, duniya ta dauki matakin watsi da wannan sana’ar musamman ganin yadda ake cin zarafin mutanen da aka yi safararsu tare da kuma ci da guminsu.

  • Wang Wenbin: Hannuwan ‘Yan Siyasar Amurka Da “‘Yan Ina Da Yaki” Na Jike Da Jinin Al’ummun Gabas Ta Tsakiya
  • Yadda Rijiya Ta Rufta Da Uba Da Ɗansa A Kano

Taken bikin na wannan shekarar shi ne yadda ake amfani da kafafen sadarwa na zamani wajen amfani da su don safarar mutane a sassan duniya da nemo hanyoyin dakile harkokin masu safarar mutane.

Majalisar dinkin Duniya ta bayar da shawarar daukar matakin fadakar da jama’a bukatar taka-tsantsan wajen amfani da kafafen sadarwa na zamani don kaucewa fadawa tarkon masu safarar mutane wadanda suke amfani da jahilcin mutane wajen cutar da su.

Ana sa ran amfani da taken na wannan shekarar don fito da dukkan hanyoyin da masu safarar mutane za su iya amfani da su wajen aiwatar da mugun aikin nasu tare da fadakar da al’umma hanyoyin kauce wa fadawa tarkon nasu.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

“Masu safarar mutane na amfani da kafafen sadarwa wajen yaudarar mutane ciki har da yara kanana, suna amfani da hanyoyi dabandaban don jawo hankalin mutane, kamar yadda Majalisar dinkin duniya ta ankarar.

“Haka kuma masu safarar mutane na amfani da sirrikan kafafen sadarwa wajen hulda a tsakanisu ba tare da al’umma sun fahimci abin da ake ciki ba suna kuma ankarar da junansu don kaucewa fadawa hannun jami’an tsaro.”

A jawabinsa na wannan ranar, Shugaban Majalisar dinkin Duniya, Antonio Guetteres, ya bayyana cewa, wadanda suka fi fadawa komar masu safarar mutane sun hada da mata da yara kanana.

“Masu safarar mutane na amfani da rauninsu ta hanyar amfani da kafofin sadarwa na zamani tare da kwarewarsu na kimiyya da fasaha wajen bibiya tare da yaudarar mutane, sukan kuma kwadaitar da su samun ayyuka a kasashen waje.”

Hukumar majalisar dinkin mai kula da masu aikata manyan laifufkka (UNODC) a rahotonta na shekarar 2018, ta bayyana cewa an samu nasarar gano akalla wadanda aka yi safarar su har mutum 50,000 da aka bayar da rahoton su a kasashe 148.

Haka kuma an fahimci cewa, kashi 50 na wadanda aka yi safarar na su ana yi ne don sanya su a sana’ar karuwanci a kasashen duniya, kashi 38 kuma ana jefa su ayyukan karfi ne ba tare da albashi ba.

An kuma gano cewa, kashi 46 daga cikin wadanda aka yi safarar nasu mata ne yayin da kuma kashi 19 kananan yara mata ne.

Daya daga cikin mutum uku daga wadanda aka yi safarar su suna kasancewa yara ne kanana yayin da kuma yawan yaran da ake safarar yana karuwa a kullum haka kuma yawan yara maza da aka yi safara su a cikin shekara 15 ya karu da kashi 5 a fadin duniya a ‘yan shekarun nan.

Majalisar ta kuma sanar da cewa, rahotanni ya nuna cewa, kashi 79 na wadanda ake safarar ana yin hakan ne don jefa su ayyukan karuwanci.

An kuma fi farauto ‘yan mata don amfani da su wanannan sana’ar. A rahotonta na shekarar 2021, hukumar yaki da safarar mutane a Nijeriya (NAPTIP), ta bayyana cewa, an samu rahoton safarar mtane har 1,112 yayin da kuma kashi 35.8 a cikin su an farauto su ne don abin da ya shafi harkar karuwanci da zama bakin haure.

Haka kuma rahoton UNDC na shekarar 2020 ya nuna cewa, kashi 60 na wadanda aka yi safarar su yankin Afrika Yamma yara ne kanana, an kuma karfafa matakai don kawo karshen wananan lamarin da gaggawa.

Yawancin masu safarar na fakewa ne da halin talauci da al’umma ke ciki ne wajen yaudarar mutane wadanda suke fafutukar tserewa daga kangin talaucin da suke fuskantar da kuma barazana na rayuwa a fannoni da dama kamar yadda kungiyar Lauyoyi Mata ta duniya (FIDA) ta bayyana a taron kwanakin baya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BincikeLeadership HausaManyan LabaraiRa'ayiRahoto
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wang Wenbin: Hannuwan ‘Yan Siyasar Amurka Da “‘Yan Ina Da Yaki” Na Jike Da Jinin Al’ummun Gabas Ta Tsakiya

Next Post

Tsadar Farashi: Yadda ‘Yan Nijeriya Suka Koma Sayen Kaya Masu Araha

Related

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

4 weeks ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

1 month ago
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Rahotonni

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

1 month ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Rahotonni

Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto

1 month ago
Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi
Rahotonni

Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi

1 month ago
Tinubu
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

2 months ago
Next Post
Tsadar Farashi: Yadda ‘Yan Nijeriya Suka Koma Sayen Kaya Masu Araha

Tsadar Farashi: Yadda 'Yan Nijeriya Suka Koma Sayen Kaya Masu Araha

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.