ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,127, Sun Sace 518 A Watan Oktoba – Rahoto

by Sadiq
2 years ago
Rahoto

Wani rahoton tsaro na wata-wata da wani kamfani mai zaman kansa na tsaro, Beacon Consulting Ltd ya fitar, ya ce a Nijeriya an samu rahotannin tsaro 935, inda mutane 1,127 suka mutu a hannun ‘yan bindiga a watan Oktoba, 2023.

Rahoton da aka fitar a ranar 15 ga watan Nuwamba, 2023, ya ce an yi garkuwa da mutane 518 a tsawon lokacin, yayin da matsalar tsaro ta kara ta’azzara idan aka kwatanta da watannin baya.

  • Nijeriya Za Ta Bayar Da Fifiko Ga Fasaha Da Makamashi Shettima
  • Yadda Za A Sake Farawa Daga Birnin San Francisco

Rahoton ya yi nazari ne kan al’amuran tsaro da suka faru a Nijeriya daga tsakanin 1 zuwa 31 ga watan Oktoban 2023.

ADVERTISEMENT

A cewar rahoton, a watan Oktoban 2023, “Nijeriya ta fuskanci matsalolin tsaro 935 wanda ke nuni da karuwar kashi 70.6 cikin 100 daga bayanan da aka fitar a watan Satumba; an samu asarar rayuka 1,127 wanda ke nuni da karuwar kashi 93.97 cikin 100, sannan an sace mutane 518 da ke wakiltar kashi 50.6 cikin 100.”

Rahoton ya kuma yi nuni da cewa yankin Arewa-maso-Gabas ne ya fi kowane yankin yawan fuskantar matsalar tsaro da asarar rayuka, da kuma sace-sacen jama’a, yayin da yankin Arewa-maso-maso-Yamma ke bi masa baya.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

Bayanai daga cibiyar tsaro ta Beacon sun nuna cewa an samu bayanan matsalar tsaro 466, kazalika an samu asarar rayuka 433, da kuma sace mutane 253 a fadin kananan hukumomi 62 da ke yankin Arewa maso Gabashin Nijeriya.

“Rikicin tsakanin ISWAP) da Jama’atu Ahlis Sunna Lidda’awati wal Jihad (JAS) ya taimaka wajen karuwar adadin.”

Rahoton ya kara da cewa an samu asarar rayuka a yankin Arewa maso Gabas.

Manajan daraktan kamfanin Beacon Consulting Limited, Dokta Kabir Adamu, ya yi karin haske game da rahoton, inda ya bayyana matsalolin rashin tsaro a Nijeriya da kuma bukatar yin amfani da tsarin da bayanan da kamfanin Beacon Consulting ke fitarwa domin inganta rayuwar daidaikun mutane da tsaron kasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba
Manyan Labarai

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

November 12, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
Next Post
An Kafa Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje 41,947 A Kasar Sin Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

An Kafa Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje 41,947 A Kasar Sin Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025
An Kafa Cibiyar Kiwon Lafiya Ta Hadin Gwiwa Ta Farko Tsakanin Sin Da Afirka A Guinea

An Kafa Cibiyar Kiwon Lafiya Ta Hadin Gwiwa Ta Farko Tsakanin Sin Da Afirka A Guinea

November 13, 2025
Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

November 13, 2025
NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

November 13, 2025
Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

November 13, 2025
Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

November 13, 2025
Nijeriya Za Ta Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Gusau

Nijeriya Za Ta Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Gusau

November 13, 2025
‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

November 13, 2025
Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

November 13, 2025
Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.