• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Sace Yara ‘Yan Makaranta 6 A Nasarawa 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
‘Yan Bindiga Sun Sace Yara ‘Yan Makaranta 6 A Nasarawa 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An samu rudani a unguwar Alwaza da ke karamar hukumar Doma a Jihar Nasarawa, yayin da aka yi garkuwa da yara ‘yan makaranta akalla shida a makarantar firamare a ranar Juma’a.

Hakan dai na zuwa ne kamar yadda rundunar ‘yansandan jihar, ta ce an sace dalibai biyu ne kawai a kan hanyarsu ta zuwa makaranta, ba dalibai shida ba.

  • Dimokuradiyya Ta Zauna Daram A Nijeriya, Ba Batun Juyin Mulki – Shugaban Tsaro
  • 2023: Manyan ‘Yan Takara Na Shafa Wa Juna Kashin Kaji

Wata majiya a unguwar da ta nemi a sakaya sunanta ta shaida wa wakilinmu cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 7:00 na safe a lokacin da sauran daliban makarantar ke ci gaba da zuwa.

Ya ce, “Ba mu taba tsammanin faruwar irin wannan abu a cikin al’ummarmu ba.

“Yaran ‘yan makarantar, kimanin shida daga cikinsu, ‘yan bindiga dauke da muggan makamai ne suka yi garkuwa da su, inda suka tafi da su inda ba a sani ba.

Labarai Masu Nasaba

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

“A matsayinmu na mazauna unguwar, ba za mu iya yin wani abu don kubutar da su ba, saboda masu laifin suna da makamai amma mun sanar da ‘yansanda halin da ake ciki kuma na yi imanin cewa za su yi kokarin kubutar da daliban da aka sace.”

A halin da ake ciki, kakakin rundunar ‘yansandan jihar, DSP Ramhan Nansel, ya karyata ikirarin cewa an yi garkuwa da wasu daliban makarantar firamaren na, Alwaza, a harabar makarantar.

Ya bayyana cewa ‘yan bindigar sun sace dalibai biyu ne kawai.

Ya ce sun hada da yara maza biyu ‘yan shekara bakwai zuwa takwas, inda suka kara da cewa suna kan hanyarsu ta zuwa makaranta ne lokacin da lamarin ya faru.

Sai dai kakakin, ya ce ‘yansanda suna samu labarin, kwamishinan ‘yansandan, Maiyaki Baba, ya jagoranci jami’an rundunar, da kungiyoyin ‘yan banga da sauran jami’an tsaro zuwa wurin da harin ya faru.

Ya ce, “Bayanan da nake samu sun ce an dauke yaran maza biyu masu shekaru daga tsakanin bakwai zuwa takwas a hanyarsu ta zuwa makaranta a makarantar firamare ta kauyen Alwaza.

“Da samun bayanan da misalin karfe 7:10 na safiyar yau, tawagar hadin guiwa karkashin jagorancin kwamishinan ‘yansanda da suka hada da ‘yansanda, sojoji da ‘yan banga suka tattaru zuwa wurin da harin ya faru domin kubutar da daliban da aka yi garkuwa da su tare da bankado wadanda wuka aikata laifin.

“Har yanzu muna kokarin gano ‘yan bindigar kuma mun yi alkawarin yin duk abin da za mu iya don magance lamarin.”

Ya yi kira ga mazauna yankin Alwaza da su ci gaba da gudanar da sana’o’insu ba tare da wata fargaba ba.

Kakakin ya yi kira da su kai rahoton duk wata fuska da ba a saba gani ba a yankin ba ga ofishin ‘yansanda mafi kusa da su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaGarkuwaNasarawaYan bindigaYara 'Yan Makaranta
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sauyin Da Ake Samu Wajen Bunkasa Lantarki A Jihar Yobe -Injiniya Goneri

Next Post

Mataimakin Shugaban Bankin Duniya: Tattalin Arzikin Sin Zai Kara Bunkasa A Bana

Related

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

7 hours ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

18 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

24 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

1 day ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

2 days ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

2 days ago
Next Post
Mataimakin Shugaban Bankin Duniya: Tattalin Arzikin Sin Zai Kara Bunkasa A Bana

Mataimakin Shugaban Bankin Duniya: Tattalin Arzikin Sin Zai Kara Bunkasa A Bana

LABARAI MASU NASABA

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.