• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Sace Yara ‘Yan Makaranta 6 A Nasarawa 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
‘Yan Bindiga Sun Sace Yara ‘Yan Makaranta 6 A Nasarawa 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An samu rudani a unguwar Alwaza da ke karamar hukumar Doma a Jihar Nasarawa, yayin da aka yi garkuwa da yara ‘yan makaranta akalla shida a makarantar firamare a ranar Juma’a.

Hakan dai na zuwa ne kamar yadda rundunar ‘yansandan jihar, ta ce an sace dalibai biyu ne kawai a kan hanyarsu ta zuwa makaranta, ba dalibai shida ba.

  • Dimokuradiyya Ta Zauna Daram A Nijeriya, Ba Batun Juyin Mulki – Shugaban Tsaro
  • 2023: Manyan ‘Yan Takara Na Shafa Wa Juna Kashin Kaji

Wata majiya a unguwar da ta nemi a sakaya sunanta ta shaida wa wakilinmu cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 7:00 na safe a lokacin da sauran daliban makarantar ke ci gaba da zuwa.

Ya ce, “Ba mu taba tsammanin faruwar irin wannan abu a cikin al’ummarmu ba.

“Yaran ‘yan makarantar, kimanin shida daga cikinsu, ‘yan bindiga dauke da muggan makamai ne suka yi garkuwa da su, inda suka tafi da su inda ba a sani ba.

Labarai Masu Nasaba

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

“A matsayinmu na mazauna unguwar, ba za mu iya yin wani abu don kubutar da su ba, saboda masu laifin suna da makamai amma mun sanar da ‘yansanda halin da ake ciki kuma na yi imanin cewa za su yi kokarin kubutar da daliban da aka sace.”

A halin da ake ciki, kakakin rundunar ‘yansandan jihar, DSP Ramhan Nansel, ya karyata ikirarin cewa an yi garkuwa da wasu daliban makarantar firamaren na, Alwaza, a harabar makarantar.

Ya bayyana cewa ‘yan bindigar sun sace dalibai biyu ne kawai.

Ya ce sun hada da yara maza biyu ‘yan shekara bakwai zuwa takwas, inda suka kara da cewa suna kan hanyarsu ta zuwa makaranta ne lokacin da lamarin ya faru.

Sai dai kakakin, ya ce ‘yansanda suna samu labarin, kwamishinan ‘yansandan, Maiyaki Baba, ya jagoranci jami’an rundunar, da kungiyoyin ‘yan banga da sauran jami’an tsaro zuwa wurin da harin ya faru.

Ya ce, “Bayanan da nake samu sun ce an dauke yaran maza biyu masu shekaru daga tsakanin bakwai zuwa takwas a hanyarsu ta zuwa makaranta a makarantar firamare ta kauyen Alwaza.

“Da samun bayanan da misalin karfe 7:10 na safiyar yau, tawagar hadin guiwa karkashin jagorancin kwamishinan ‘yansanda da suka hada da ‘yansanda, sojoji da ‘yan banga suka tattaru zuwa wurin da harin ya faru domin kubutar da daliban da aka yi garkuwa da su tare da bankado wadanda wuka aikata laifin.

“Har yanzu muna kokarin gano ‘yan bindigar kuma mun yi alkawarin yin duk abin da za mu iya don magance lamarin.”

Ya yi kira ga mazauna yankin Alwaza da su ci gaba da gudanar da sana’o’insu ba tare da wata fargaba ba.

Kakakin ya yi kira da su kai rahoton duk wata fuska da ba a saba gani ba a yankin ba ga ofishin ‘yansanda mafi kusa da su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaGarkuwaNasarawaYan bindigaYara 'Yan Makaranta
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sauyin Da Ake Samu Wajen Bunkasa Lantarki A Jihar Yobe -Injiniya Goneri

Next Post

Mataimakin Shugaban Bankin Duniya: Tattalin Arzikin Sin Zai Kara Bunkasa A Bana

Related

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

6 hours ago
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

11 hours ago
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

15 hours ago
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

15 hours ago
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

16 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

19 hours ago
Next Post
Mataimakin Shugaban Bankin Duniya: Tattalin Arzikin Sin Zai Kara Bunkasa A Bana

Mataimakin Shugaban Bankin Duniya: Tattalin Arzikin Sin Zai Kara Bunkasa A Bana

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.