ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Sace Yara ‘Yan Makaranta 6 A Nasarawa 

by Sadiq
3 years ago
Yara

An samu rudani a unguwar Alwaza da ke karamar hukumar Doma a Jihar Nasarawa, yayin da aka yi garkuwa da yara ‘yan makaranta akalla shida a makarantar firamare a ranar Juma’a.

Hakan dai na zuwa ne kamar yadda rundunar ‘yansandan jihar, ta ce an sace dalibai biyu ne kawai a kan hanyarsu ta zuwa makaranta, ba dalibai shida ba.

  • Dimokuradiyya Ta Zauna Daram A Nijeriya, Ba Batun Juyin Mulki – Shugaban Tsaro
  • 2023: Manyan ‘Yan Takara Na Shafa Wa Juna Kashin Kaji

Wata majiya a unguwar da ta nemi a sakaya sunanta ta shaida wa wakilinmu cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 7:00 na safe a lokacin da sauran daliban makarantar ke ci gaba da zuwa.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Ba mu taba tsammanin faruwar irin wannan abu a cikin al’ummarmu ba.

“Yaran ‘yan makarantar, kimanin shida daga cikinsu, ‘yan bindiga dauke da muggan makamai ne suka yi garkuwa da su, inda suka tafi da su inda ba a sani ba.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

“A matsayinmu na mazauna unguwar, ba za mu iya yin wani abu don kubutar da su ba, saboda masu laifin suna da makamai amma mun sanar da ‘yansanda halin da ake ciki kuma na yi imanin cewa za su yi kokarin kubutar da daliban da aka sace.”

A halin da ake ciki, kakakin rundunar ‘yansandan jihar, DSP Ramhan Nansel, ya karyata ikirarin cewa an yi garkuwa da wasu daliban makarantar firamaren na, Alwaza, a harabar makarantar.

Ya bayyana cewa ‘yan bindigar sun sace dalibai biyu ne kawai.

Ya ce sun hada da yara maza biyu ‘yan shekara bakwai zuwa takwas, inda suka kara da cewa suna kan hanyarsu ta zuwa makaranta ne lokacin da lamarin ya faru.

Sai dai kakakin, ya ce ‘yansanda suna samu labarin, kwamishinan ‘yansandan, Maiyaki Baba, ya jagoranci jami’an rundunar, da kungiyoyin ‘yan banga da sauran jami’an tsaro zuwa wurin da harin ya faru.

Ya ce, “Bayanan da nake samu sun ce an dauke yaran maza biyu masu shekaru daga tsakanin bakwai zuwa takwas a hanyarsu ta zuwa makaranta a makarantar firamare ta kauyen Alwaza.

“Da samun bayanan da misalin karfe 7:10 na safiyar yau, tawagar hadin guiwa karkashin jagorancin kwamishinan ‘yansanda da suka hada da ‘yansanda, sojoji da ‘yan banga suka tattaru zuwa wurin da harin ya faru domin kubutar da daliban da aka yi garkuwa da su tare da bankado wadanda wuka aikata laifin.

“Har yanzu muna kokarin gano ‘yan bindigar kuma mun yi alkawarin yin duk abin da za mu iya don magance lamarin.”

Ya yi kira ga mazauna yankin Alwaza da su ci gaba da gudanar da sana’o’insu ba tare da wata fargaba ba.

Kakakin ya yi kira da su kai rahoton duk wata fuska da ba a saba gani ba a yankin ba ga ofishin ‘yansanda mafi kusa da su.

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Next Post
Mataimakin Shugaban Bankin Duniya: Tattalin Arzikin Sin Zai Kara Bunkasa A Bana

Mataimakin Shugaban Bankin Duniya: Tattalin Arzikin Sin Zai Kara Bunkasa A Bana

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.