• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga: ‘Yansanda Sun Kwato Shanu 500 Da Babura 8 A Neja 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
‘Yan Bindiga: ‘Yansanda Sun Kwato Shanu 500 Da Babura 8 A Neja 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansandan Jihar Neja ta kwato shanu akalla 500 da babura takwas da ‘yan bindiga suka kwace a yayin wata musayar wuta da suka yi daga wasu kananan hukumomi uku na jihar. 

Kananan hukumomin sun hada da Paikoro, Munya da Wushishi.

  1. Kurar Sauya Fasalin Kudi: ‘Mahaukatan’ Sayen-sayen Da Masu Boye Kudi Ke Yi
  2. Hadin Gwiwar Sin Da Afrika Kan Tattalin Arzikin Zamani Ya Baiwa Afrika Damammaki Masu Kyau

Rundunar, a cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yansandan jihar, DSP Wasiu Abiodun, ya sanya wa hannu, ta ce jami’an rundunar sun samu nasarar dakile dukkanin hare-haren.

Ya ce a ranar Laraba wasu da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne suka kai farmaki kauyen Kaffin-Koro da ke karamar hukumar Paikoro, ta kauyen Adunu, inda suka rika harbe-harbe ba tare da bata lokaci ba, kuma a cikin haka ne wasu mutane biyu suka samu raunuka harsashi yayin da aka yi awon gaba da wasu shanu.

‘Yan bindigar sun yi watsi da shanun da aka sace, yayin da aka kai wadanda suka jikkata zuwa asibitin Janar na Kaffin-Koro kuma suna karbar magani”.

Labarai Masu Nasaba

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

A cewar rundunar ‘yansandan a ranar Litinin din da ta gabata ne wasu ‘yan bindiga suka yi awon gaba da wasu shanu da ba a tantance adadinsu ba daga garuruwan Akare, Jiwawa, Gulanji, Kadaura, da wasu kauyuka da ke makwabtaka da Wushishi suna kokarin tsallakawa hanyar Tegina zuwa Zungeru tsakanin kauyukan Garun-Gabas da Yakila.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Rundunar ‘yansanda d sojoji sun hada kai tare da mayar da martani cikin gaggawa inda suka yi artabu da ‘yan bindigar.

“Sakamakon haka ‘yan bindigar sun yi watsi da shanun da suka sace da wasu babura a yayin da suka shiga cikin rudani domin tsira da raunukan harbin bindiga a dajin.

Abiodun ya kara da cewa, a ranar Litinin din da ta gabata ne wasu ‘yan bindiga dauke da makamai suka kai hari kauyen Chibani ta gundumar Kuchi ta karamar hukumar Munya, yayin da jami’an ‘yansanda da jami’an ‘yan banga suka tattaru zuwa yankin inda suka yi artabu da ‘yan bindigar.

Ya kara da cewa, “An samu nasarar fatattakar ‘yan bindigar, inda suka yi watsi da shanun, yayin da suka tsere ta Kauyen Rishi Kaduna.

Sai dai wasu mutane biyu daga cikin ‘yan banga na yankin sun rasa rayukansu a yayin artabu da bindigar.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaArtabuMusayar WutaNejaShanuYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Tana Goyon Bayan Bukatar Kasashe Masu Tasowa Game Da Kudaden Tallafin Sauyin Yanayi

Next Post

Bikin CIIE Na Haifar Da Moriya Ga Duniya

Related

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

6 hours ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

9 hours ago
Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka
Manyan Labarai

Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

16 hours ago
Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 
Manyan Labarai

Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

20 hours ago
Safarar Yara: Gwamnatin Adamawa Ta Haɗa Yara 14 Da Iyayensu Da Aka Ceto A Anambra 
Manyan Labarai

Safarar Yara: Gwamnatin Adamawa Ta Haɗa Yara 14 Da Iyayensu Da Aka Ceto A Anambra 

1 day ago
Hare-hare: Adadin Mutanen Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe A Katsina Ya Haura 50
Manyan Labarai

Hare-hare: Adadin Mutanen Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe A Katsina Ya Haura 50

2 days ago
Next Post
Bikin CIIE Na Haifar Da Moriya Ga Duniya

Bikin CIIE Na Haifar Da Moriya Ga Duniya

LABARAI MASU NASABA

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

August 21, 2025
Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

August 21, 2025
Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

August 21, 2025
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

August 21, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

August 21, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

August 21, 2025
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

August 21, 2025
Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.