ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwar Sin Da Afrika Kan Tattalin Arzikin Zamani Ya Baiwa Afrika Damammaki Masu Kyau

by CMG Hausa
4 years ago
Afrika

Abokai, yanzu ana gudanar da babban taron yanar gizo na duniya a kasar Sin. Bunkasuwar Sin a wannan fanni ya amfanawa duk fadin duniya. Yau “duniya a zanen MINA” zai yi muku bayani kan ma’anar hadin kan Sin da Afrika a fannin tattalin arzikin yanar gizo.

Taron da ake gudanarwa a birnin Yiwu dake lardin Zhejiang ya samu halartar wakilai fiye da 2000 daga kasa da kasa, kuma babban abin da ake tattaunawa a taron shi ne hadin kai da samun ci gaba tare.

  • Guterres Ya Yaba Wa Kasar Sin Kan Yadda Take Kokarin Tinkarar Sauyin Yanayi

Bisa kididdigar da hukumar kula da masana’antu da sadarwa ta kasar Sin ta bayar, an ce, yanzu Sin ta kulla yarjejeniyar fahimtar juna tsakaninta da kasashe 17 dake kan hanyar siliki ta fannin yanar gizo, kuma ta kafa tsarin hadin gwiwa da kasashe 23 dake kan wannan hanya a fannin kasuwanci ta yanar gizo.

ADVERTISEMENT

Alkaluman da kwamitin kula da sadarwa na Najeriya ya bayar, sun yi nuni da cewa, ya zuwa watan Yuni na bana, yawan mutanen dake kama Intanet ya haura miliyan 150, wato kaso 70% na al’ummar kasar na samun hidimar yanar gizo. Irin wadannan sauye-sauye da aka samu ba su rabuwa da ababen more rayuwa da kamfanonin Sin ke taimakawa wajen gina su a kasar ta fannin yanar gizo.

Cikin ‘yan shekarun baya, kamfanonin Sin sun himmantu wajen kafa na’urorin yanar gizo a Afrika. Alal misali, zuwa karshen watan Oktomba da ya wuce, kamfanin ZTE na kasar Sin ya baiwa ‘yan Afrika fiye da miliyan 400 hidimar yanar gizo, ta hanyar gina na’urorin yanar gizo.

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Yanzu ana iya samun sadawar 5G a nahiyar Afrika, matakin da ya baiwa tattalin arzikin yanar gizo tushen samun bunkasuwa mai kyau, shi ya sa mutane da dama suka samu arziki ta hanyar dogaro da yanar gizo.

Wata takardar bayani kan bunkasuwar tattalin arzikin yanar gizo a Afrika da aka fitar a watan Mayun bana ta yi nuni da cewa, a shekarar 2019 yawan mutanen da suka kama ayyukan da suka shafi cinikayyar yanar gizo ya karu zuwa miliyan 233, adadin da kuma zai kai miliyan 478 kafin shekarar 2024.

Hadin kan Sin da Afrika a wannan fanni mai habaka, ya kuma ingiza cinikayyar Sin da Afrika zuwa gaba. Bisa alkaluman da aka bayar, an ce, yawan kudin dake shafar cinikin bangarorin biyu ya karu da kashi 35% a shekarar bara, kuma tattalin arzikin yanar gizo ya zama sabuwar hanyar kawar da talauci a nahiyar Afirka.

A halin yanzu, kasashen Afrika da dama na sa ran yin hadin gwiwa da kasar Sin a fannin tattalin arzikin yanar gizo, hakan ya sa wasu kamfanoni masu karfi na kasar Sin a wannan fanni suka hada kai da kasashen Afrika ciki hadda Najeriya, don taimaka musu wajen samun ci gaba dangane da tattalin arzikin yanar gizo a fannin hada-hadar kudi da ciniki ta yanar gizo da sufurin kayayyaki da sauransu.

Nahiyar Afrika na da kasashe maras ci gaba mafi yawa a duniya, kuma yadda kasar Sin ta ba da taimakon ingiza bunkasuwarsu bisa hadin gwiwar tattalin arzikin yanar gizo, ba shakka zai samar da sabbin damammaki masu kyau ga nahiyar wajen kawar da talauci, baya ga haka zai ingiza bunkasuwar tattalin arizkin duniya gaba daya. (Mai zane kuma rubuta: MINA)

Afrika
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Daga Birnin Sin

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
Daga Birnin Sin

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Next Post
INEC Ta Samar Da Tsarin Yadda ‘Yan Gudun Hijira Za Su Yi Zabe A Zamfara

INEC Ta Samar Da Tsarin Yadda 'Yan Gudun Hijira Za Su Yi Zabe A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.