ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwar Sin Da Afrika Kan Tattalin Arzikin Zamani Ya Baiwa Afrika Damammaki Masu Kyau

by CMG Hausa
4 years ago
Afrika

Abokai, yanzu ana gudanar da babban taron yanar gizo na duniya a kasar Sin. Bunkasuwar Sin a wannan fanni ya amfanawa duk fadin duniya. Yau “duniya a zanen MINA” zai yi muku bayani kan ma’anar hadin kan Sin da Afrika a fannin tattalin arzikin yanar gizo.

Taron da ake gudanarwa a birnin Yiwu dake lardin Zhejiang ya samu halartar wakilai fiye da 2000 daga kasa da kasa, kuma babban abin da ake tattaunawa a taron shi ne hadin kai da samun ci gaba tare.

  • Guterres Ya Yaba Wa Kasar Sin Kan Yadda Take Kokarin Tinkarar Sauyin Yanayi

Bisa kididdigar da hukumar kula da masana’antu da sadarwa ta kasar Sin ta bayar, an ce, yanzu Sin ta kulla yarjejeniyar fahimtar juna tsakaninta da kasashe 17 dake kan hanyar siliki ta fannin yanar gizo, kuma ta kafa tsarin hadin gwiwa da kasashe 23 dake kan wannan hanya a fannin kasuwanci ta yanar gizo.

ADVERTISEMENT

Alkaluman da kwamitin kula da sadarwa na Najeriya ya bayar, sun yi nuni da cewa, ya zuwa watan Yuni na bana, yawan mutanen dake kama Intanet ya haura miliyan 150, wato kaso 70% na al’ummar kasar na samun hidimar yanar gizo. Irin wadannan sauye-sauye da aka samu ba su rabuwa da ababen more rayuwa da kamfanonin Sin ke taimakawa wajen gina su a kasar ta fannin yanar gizo.

Cikin ‘yan shekarun baya, kamfanonin Sin sun himmantu wajen kafa na’urorin yanar gizo a Afrika. Alal misali, zuwa karshen watan Oktomba da ya wuce, kamfanin ZTE na kasar Sin ya baiwa ‘yan Afrika fiye da miliyan 400 hidimar yanar gizo, ta hanyar gina na’urorin yanar gizo.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Yanzu ana iya samun sadawar 5G a nahiyar Afrika, matakin da ya baiwa tattalin arzikin yanar gizo tushen samun bunkasuwa mai kyau, shi ya sa mutane da dama suka samu arziki ta hanyar dogaro da yanar gizo.

Wata takardar bayani kan bunkasuwar tattalin arzikin yanar gizo a Afrika da aka fitar a watan Mayun bana ta yi nuni da cewa, a shekarar 2019 yawan mutanen da suka kama ayyukan da suka shafi cinikayyar yanar gizo ya karu zuwa miliyan 233, adadin da kuma zai kai miliyan 478 kafin shekarar 2024.

Hadin kan Sin da Afrika a wannan fanni mai habaka, ya kuma ingiza cinikayyar Sin da Afrika zuwa gaba. Bisa alkaluman da aka bayar, an ce, yawan kudin dake shafar cinikin bangarorin biyu ya karu da kashi 35% a shekarar bara, kuma tattalin arzikin yanar gizo ya zama sabuwar hanyar kawar da talauci a nahiyar Afirka.

A halin yanzu, kasashen Afrika da dama na sa ran yin hadin gwiwa da kasar Sin a fannin tattalin arzikin yanar gizo, hakan ya sa wasu kamfanoni masu karfi na kasar Sin a wannan fanni suka hada kai da kasashen Afrika ciki hadda Najeriya, don taimaka musu wajen samun ci gaba dangane da tattalin arzikin yanar gizo a fannin hada-hadar kudi da ciniki ta yanar gizo da sufurin kayayyaki da sauransu.

Nahiyar Afrika na da kasashe maras ci gaba mafi yawa a duniya, kuma yadda kasar Sin ta ba da taimakon ingiza bunkasuwarsu bisa hadin gwiwar tattalin arzikin yanar gizo, ba shakka zai samar da sabbin damammaki masu kyau ga nahiyar wajen kawar da talauci, baya ga haka zai ingiza bunkasuwar tattalin arizkin duniya gaba daya. (Mai zane kuma rubuta: MINA)

Afrika
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
INEC Ta Samar Da Tsarin Yadda ‘Yan Gudun Hijira Za Su Yi Zabe A Zamfara

INEC Ta Samar Da Tsarin Yadda 'Yan Gudun Hijira Za Su Yi Zabe A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.