• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

 ‘Yan Majalisar Nijeriya Na Matsin Lamba Ga Jami’an Gwamnati Wajen Yin Cushe A Kasafin Kudi –Jega

by Yusuf Shuaibu
9 months ago
in Siyasa
0
 ‘Yan Majalisar Nijeriya Na Matsin Lamba Ga Jami’an Gwamnati Wajen Yin Cushe A Kasafin Kudi –Jega
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Farfesa Attahiru Jega, ya bayyana cewa ‘yan majalisan Nijereiya na matsinlamba ga jami’an gwamnati wajen yin cushe a kasafin kudi domin cimma burinsu.

Farfesa Jega ya bayyana haka ne a jawabin da ya gabatar a taron ‘Horar da canjin dabi’un cin hanci da ’, wanda hukumar yaki da cin hanci da rashawa da sauran laifuka (ICPC) ta shirya a Abuja.

  • Ka Yi Murabus Yanzu Ko Mu Tsige Ka – ‘Yan Majalisa Ga Kakakin Majalisar Bauchi
  • Shugaban Majisar Dattawa Ya Yi Wa Daurarru 15 Afuwa Daga Gidan Yari Na Yobe

Ya bayyana cin hanci da rashawa a ma’aikatun gwamnati a matsayin babban cikas ga ci gaban Nijeriya tare da sukar matsalolin da manyan jami’ai ke fuskanta musamman daga bangaren majalisa.

“Akwai mutanen da suke tursasa jami’an gwamnati su gudanar da aikinsu, ko mai kyau ko kuma akasin haka. Wadannan mutane za su iya kasancewa ‘yan majalisa ko kuma ba ‘yan majalisa ba,” in ji shi.

Ya tunatar da yadda wasu ‘yan majalisar suka yi yunkurin yin tasiri a kan kasafin kudi da kuma tabbatar da kwangiloli, wanda hakan ya kawo cikas ga kokarin jami’an gwamnati na tabbatar da gaskiya.

Labarai Masu Nasaba

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Da yake waiwayar zamansa a hukumar ta INEC, ya bayyana hakan a matsayin za zakaran gwaji dafi ganin yadda ‘yan majalisar ke takurawa kan kasafin kudin hukumar da kwangiloli a kullum.

“Kaurace wa matsinlambar yana bukatar jajircewa. Yana da muhimmanci a kaurace masa don bin bin doka da ka’idojin Nijeriya.”

Ya kuma soki al’adar cin hanci da rashawa da ta yadu a sassan gwamnati tare da yin kira da a sake fasalin hukumomi.

Ana dai zargin majalisar dokokin kasar da cin hanci da rashawa daban-daban da suka hada da karkatar da kasafin kudi na tsawon shekaru. Gudanar da ayyukan mazabu babban misali ne kan hakan.

Wasu rahotannin da hukumar ICPC ta fitar sun bankado yadda ‘yan majalisar dokokin kasar ke amfani da kudaden gwamnati tare da hadin gwiwar hukumomin gwamnati ta hanyar kashe kasafin kudin kasa na ayyukan mazabu wadanda galibinsu ba su ba a aiwatar da su ba.

Rahotannin da ke bin diddigin ayyukan mazabar da ICPC ta fitar sun bankado wasu laifukan da ake zargin ‘yan majalisar tarayya na aikatawa tare da hadin gwiwar wasu jami’an ma’aikatu da hukumomin gwamnatin tarayya.

Farfesa Jega ya jaddada bukatar samun kwakkwaran jagoranci wajen magance cin hanci da rashawa.

Ya kara da cewa idan ba a samu cikakken sauye-sauye a bangaren shari’a da sauran manyan cibiyoyi ba, cin hanci da rashawa zai ci gaba da wanzuwa. Ya ce al’adar cin hanci da rashawa ta kafu ne ta hanyar lakabin gargajiya da ake ba wa jami’an gwamnati, wanda a ganinsa yana karfafa yin biyayya da ayyukan da ba su dace ba.

“Da zarar an fara yin shit un yana karami, yana ci gaba da girma, ina ba da shawarar sake duba yadda tsarin aikin gwamnati ya tasiri.”

Ya kuma jaddada bukatar karfafa kariya ga masu fallasa bayanan sirri da inganta hanyoyin karfafawa mutane kai rahoton cin hanci da rashawa.

Jega ya bayar da shawarwari da suka hada da kakkarfan kariya ga masu fallasa bayanai, hada kai da matasa, da habaka horar sabbin dabi’un shugabanci.

Da yake goyon bayan bayanan Jega, shugaban ICPC, Musa Aliyu ya bukaci shugabannin ma’aikatun tarayya, sassan da hukumomi da su karfafa tsarin yaki da cin hanci da rashawa.

Ya yi gargadin cewa rashin yin hakan zai sa a gudanar da bincike tare da gurfanar da su gaban kuliya.

“Ba za a iya kididdiga barnar da cin hanci da rashawa ya yi wa ma’aikatan gwamnati da kuma al’ummarmu ba,” in ji Aliyu, yana mai bukatar jajircewa wajen yaki da cin hanci da rashawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan Majalisa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yara Miliyan 1 Ke Mutuwa Duk Shekara A Farkon Watansu Na Haihuwa A Nijeriya – UNICEF

Next Post

Masu Harkar PoS Sun Bayyana Dalilin Karin Kudin Cire Kudi

Related

Labarai

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

1 day ago
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

2 days ago
Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 
Siyasa

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

4 days ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

5 days ago
Hoton Kwankwaso da Ganduje da Shekarau
Bakon Marubuci

Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar

6 days ago
Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ci Amanar Kano, Babu Batun Haɗin Guiwa Tsakaninsa Da Kwankwaso A 2027 – Galadima

7 days ago
Next Post
Masu Harkar PoS Sun Bayyana Dalilin Karin Kudin Cire Kudi

Masu Harkar PoS Sun Bayyana Dalilin Karin Kudin Cire Kudi

LABARAI MASU NASABA

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

August 26, 2025
An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.