• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

 ‘Yan Majalisar Nijeriya Na Matsin Lamba Ga Jami’an Gwamnati Wajen Yin Cushe A Kasafin Kudi –Jega

by Yusuf Shuaibu
7 months ago
in Siyasa
0
 ‘Yan Majalisar Nijeriya Na Matsin Lamba Ga Jami’an Gwamnati Wajen Yin Cushe A Kasafin Kudi –Jega
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Farfesa Attahiru Jega, ya bayyana cewa ‘yan majalisan Nijereiya na matsinlamba ga jami’an gwamnati wajen yin cushe a kasafin kudi domin cimma burinsu.

Farfesa Jega ya bayyana haka ne a jawabin da ya gabatar a taron ‘Horar da canjin dabi’un cin hanci da ’, wanda hukumar yaki da cin hanci da rashawa da sauran laifuka (ICPC) ta shirya a Abuja.

  • Ka Yi Murabus Yanzu Ko Mu Tsige Ka – ‘Yan Majalisa Ga Kakakin Majalisar Bauchi
  • Shugaban Majisar Dattawa Ya Yi Wa Daurarru 15 Afuwa Daga Gidan Yari Na Yobe

Ya bayyana cin hanci da rashawa a ma’aikatun gwamnati a matsayin babban cikas ga ci gaban Nijeriya tare da sukar matsalolin da manyan jami’ai ke fuskanta musamman daga bangaren majalisa.

“Akwai mutanen da suke tursasa jami’an gwamnati su gudanar da aikinsu, ko mai kyau ko kuma akasin haka. Wadannan mutane za su iya kasancewa ‘yan majalisa ko kuma ba ‘yan majalisa ba,” in ji shi.

Ya tunatar da yadda wasu ‘yan majalisar suka yi yunkurin yin tasiri a kan kasafin kudi da kuma tabbatar da kwangiloli, wanda hakan ya kawo cikas ga kokarin jami’an gwamnati na tabbatar da gaskiya.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

Da yake waiwayar zamansa a hukumar ta INEC, ya bayyana hakan a matsayin za zakaran gwaji dafi ganin yadda ‘yan majalisar ke takurawa kan kasafin kudin hukumar da kwangiloli a kullum.

“Kaurace wa matsinlambar yana bukatar jajircewa. Yana da muhimmanci a kaurace masa don bin bin doka da ka’idojin Nijeriya.”

Ya kuma soki al’adar cin hanci da rashawa da ta yadu a sassan gwamnati tare da yin kira da a sake fasalin hukumomi.

Ana dai zargin majalisar dokokin kasar da cin hanci da rashawa daban-daban da suka hada da karkatar da kasafin kudi na tsawon shekaru. Gudanar da ayyukan mazabu babban misali ne kan hakan.

Wasu rahotannin da hukumar ICPC ta fitar sun bankado yadda ‘yan majalisar dokokin kasar ke amfani da kudaden gwamnati tare da hadin gwiwar hukumomin gwamnati ta hanyar kashe kasafin kudin kasa na ayyukan mazabu wadanda galibinsu ba su ba a aiwatar da su ba.

Rahotannin da ke bin diddigin ayyukan mazabar da ICPC ta fitar sun bankado wasu laifukan da ake zargin ‘yan majalisar tarayya na aikatawa tare da hadin gwiwar wasu jami’an ma’aikatu da hukumomin gwamnatin tarayya.

Farfesa Jega ya jaddada bukatar samun kwakkwaran jagoranci wajen magance cin hanci da rashawa.

Ya kara da cewa idan ba a samu cikakken sauye-sauye a bangaren shari’a da sauran manyan cibiyoyi ba, cin hanci da rashawa zai ci gaba da wanzuwa. Ya ce al’adar cin hanci da rashawa ta kafu ne ta hanyar lakabin gargajiya da ake ba wa jami’an gwamnati, wanda a ganinsa yana karfafa yin biyayya da ayyukan da ba su dace ba.

“Da zarar an fara yin shit un yana karami, yana ci gaba da girma, ina ba da shawarar sake duba yadda tsarin aikin gwamnati ya tasiri.”

Ya kuma jaddada bukatar karfafa kariya ga masu fallasa bayanan sirri da inganta hanyoyin karfafawa mutane kai rahoton cin hanci da rashawa.

Jega ya bayar da shawarwari da suka hada da kakkarfan kariya ga masu fallasa bayanai, hada kai da matasa, da habaka horar sabbin dabi’un shugabanci.

Da yake goyon bayan bayanan Jega, shugaban ICPC, Musa Aliyu ya bukaci shugabannin ma’aikatun tarayya, sassan da hukumomi da su karfafa tsarin yaki da cin hanci da rashawa.

Ya yi gargadin cewa rashin yin hakan zai sa a gudanar da bincike tare da gurfanar da su gaban kuliya.

“Ba za a iya kididdiga barnar da cin hanci da rashawa ya yi wa ma’aikatan gwamnati da kuma al’ummarmu ba,” in ji Aliyu, yana mai bukatar jajircewa wajen yaki da cin hanci da rashawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan Majalisa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yara Miliyan 1 Ke Mutuwa Duk Shekara A Farkon Watansu Na Haihuwa A Nijeriya – UNICEF

Next Post

Masu Harkar PoS Sun Bayyana Dalilin Karin Kudin Cire Kudi

Related

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC
Manyan Labarai

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

11 hours ago
An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027
Siyasa

An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

1 day ago
Gwamnan Abba Kabir Yusuf tare da Arch. Ali Hassan
Tattaunawa

Abba Ya Dace Ya Zama Gwamnan Kano Na Har Abada Ba Shekaru 8 Kaɗai Ba – Arch Ali Hassan

2 days ago
2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega
Siyasa

2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

2 days ago
Ƴansanda Sun Gargaɗi Masu Lalata Fastar Tinubu A Kano
Siyasa

Ƴansanda Sun Gargaɗi Masu Lalata Fastar Tinubu A Kano

4 days ago
Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista
Manyan Labarai

Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista

4 days ago
Next Post
Masu Harkar PoS Sun Bayyana Dalilin Karin Kudin Cire Kudi

Masu Harkar PoS Sun Bayyana Dalilin Karin Kudin Cire Kudi

LABARAI MASU NASABA

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

June 24, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

June 24, 2025
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

June 24, 2025
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

June 24, 2025
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

June 24, 2025
Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

June 24, 2025
Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

June 24, 2025
Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

June 24, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

June 24, 2025
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.