• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Sanda Sun Kashe Dan Bindiga, Sun Kwato AK-47 A Zamfara

by Sadiq
3 years ago
'Yan Bindiga

Jami’an ‘yan sanda a Jihar Zamfara sun kashe wani dan bindiga tare da kwato bindiga kirar AK 47 da alburusai 18 a wani artabu da suka yi a kauyukan Saran Gamawa da Anguwar Mata da ke Karamar Hukumar Gummi a Jihar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin  rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara, SP Muhammad Shehu, ya fitar a Gusau ranar a Litinin.

  • Za A Shafe Shekaru Kafin A Kawo Karshen Yakin Ukraine Da Rasha —NATO
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Coci, Sun Kashe Mutane 3 A Kaduna

“A ranar 19 ga Yuni, 2022, jami’an ‘yan sandan da aka tura ta hanyar Gummi/Bukkuyum, sun samu kiran gaggawa cewa, ‘yan ta’adda dauke da makamai a kan babura sun kai farmaki Saran Gamawa da kauyukan Unguwar Mata da ke makwabtaka da su da nufin sace mutanen da ba su ji ba ba su gani ba.

“Rundunar ‘yan sanda tare da hadin gwiwar ‘yan banga na kauyukan da lamarin ya shafa, sun hada karfi da karfe tare wajen yakar ‘yan ta’addan a wani kazamin artabu da aka dauki tsawon sa’o’i ana yi.

“Sakamakon haka, daya daga cikin ‘yan ta’addan ya samu munanan raunuka, an samu bindiga kirar Ak 47 a wajen dan bindigar, yayin da wasu da dama suka tsere cikin dajin da raunukan harbin bindiga daban-daban,” in ji Shehu.

LABARAI MASU NASABA

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Ayuba Elkanah, ya yaba da jajircewar da ‘yan sandan suka yi, ya kuma bukace su da kada su yi kasa a gwiwa wajen ganin rundunar ta kare rayuka da dukiyoyin mutanen da ba su ji ba ba su gani ba a jihar.

Elkanah ya kuma umarci Kwamandan yankin Anka da DPO da ke makwabtaka da su tura tawagar hadin gwiwa don ci gaba da sintiri don dakile ci gaba da kai hare-hare a kan al’ummomin da ke yankunan.

Ya ce rundunar ta kuma tura domin ceto mutanen biyu da maharan suka yi garkuwa da su kafin isowar ‘yan sanda.

“Yayin da yake tabbatar da kudurin rundunar na kare rayuka da dukiyoyi a jihar, ya yi kira ga jama’a da su ba ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro hadin kai a kokarin kawar da ‘yan bindiga a jihar,” in ji kakakin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump
Manyan Labarai

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

November 7, 2025
Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 
Manyan Labarai

Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 

November 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Next Post
Ganduje Ya Nada Baffa A Matsayin Shugaban Hukumar Kare Hakkin Masu Siye Da Siyarwa 

Ganduje Ya Nada Baffa A Matsayin Shugaban Hukumar Kare Hakkin Masu Siye Da Siyarwa 

LABARAI MASU NASABA

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

November 7, 2025
Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 

Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 

November 7, 2025
An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

November 6, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.