• English
  • Business News
Wednesday, July 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Sanda Sun Kashe Dan Bindiga, Sun Kwato AK-47 A Zamfara

by Sadiq
3 years ago
in Labarai
0
‘Yan Sanda Sun Kashe Dan Bindiga, Sun Kwato AK-47 A Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’an ‘yan sanda a Jihar Zamfara sun kashe wani dan bindiga tare da kwato bindiga kirar AK 47 da alburusai 18 a wani artabu da suka yi a kauyukan Saran Gamawa da Anguwar Mata da ke Karamar Hukumar Gummi a Jihar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin  rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara, SP Muhammad Shehu, ya fitar a Gusau ranar a Litinin.

  • Za A Shafe Shekaru Kafin A Kawo Karshen Yakin Ukraine Da Rasha —NATO
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Coci, Sun Kashe Mutane 3 A Kaduna

“A ranar 19 ga Yuni, 2022, jami’an ‘yan sandan da aka tura ta hanyar Gummi/Bukkuyum, sun samu kiran gaggawa cewa, ‘yan ta’adda dauke da makamai a kan babura sun kai farmaki Saran Gamawa da kauyukan Unguwar Mata da ke makwabtaka da su da nufin sace mutanen da ba su ji ba ba su gani ba.

“Rundunar ‘yan sanda tare da hadin gwiwar ‘yan banga na kauyukan da lamarin ya shafa, sun hada karfi da karfe tare wajen yakar ‘yan ta’addan a wani kazamin artabu da aka dauki tsawon sa’o’i ana yi.

“Sakamakon haka, daya daga cikin ‘yan ta’addan ya samu munanan raunuka, an samu bindiga kirar Ak 47 a wajen dan bindigar, yayin da wasu da dama suka tsere cikin dajin da raunukan harbin bindiga daban-daban,” in ji Shehu.

Labarai Masu Nasaba

Kwankwaso  Ne Kaɗai Ɗan Siyasar Da Zai Iya Maye Gurbin Buhari — Jigo A NNPP

Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Ayuba Elkanah, ya yaba da jajircewar da ‘yan sandan suka yi, ya kuma bukace su da kada su yi kasa a gwiwa wajen ganin rundunar ta kare rayuka da dukiyoyin mutanen da ba su ji ba ba su gani ba a jihar.

Elkanah ya kuma umarci Kwamandan yankin Anka da DPO da ke makwabtaka da su tura tawagar hadin gwiwa don ci gaba da sintiri don dakile ci gaba da kai hare-hare a kan al’ummomin da ke yankunan.

Ya ce rundunar ta kuma tura domin ceto mutanen biyu da maharan suka yi garkuwa da su kafin isowar ‘yan sanda.

“Yayin da yake tabbatar da kudurin rundunar na kare rayuka da dukiyoyi a jihar, ya yi kira ga jama’a da su ba ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro hadin kai a kokarin kawar da ‘yan bindiga a jihar,” in ji kakakin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan SandaArtabuDan BindigaYan bindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Za A Shafe Shekaru Kafin A Kawo Karshen Yakin Ukraine Da Rasha —NATO

Next Post

Ganduje Ya Nada Baffa A Matsayin Shugaban Hukumar Kare Hakkin Masu Siye Da Siyarwa 

Related

Kwankwaso  Ne Kaɗai Ɗan Siyasar Da Zai Iya Maye Gurbin Buhari — Jigo A NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso  Ne Kaɗai Ɗan Siyasar Da Zai Iya Maye Gurbin Buhari — Jigo A NNPP

4 hours ago
Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO
Labarai

Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO

5 hours ago
Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

6 hours ago
Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaddamar Da Kwaskwarimar Majalisar Dokoki Kan Naira Biliyan 7
Manyan Labarai

Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaddamar Da Kwaskwarimar Majalisar Dokoki Kan Naira Biliyan 7

7 hours ago
Yanzu-Yanzu: Majalisa Ta Amince Wa Tinubu Ciwo Bashin Dala Biliyan 21
Manyan Labarai

Yanzu-Yanzu: Majalisa Ta Amince Wa Tinubu Ciwo Bashin Dala Biliyan 21

10 hours ago
Natasha Ta Koma Majalisar Dattawa Duk Da Tsaurara Tsaro
Manyan Labarai

Natasha Ta Koma Majalisar Dattawa Duk Da Tsaurara Tsaro

13 hours ago
Next Post
Ganduje Ya Nada Baffa A Matsayin Shugaban Hukumar Kare Hakkin Masu Siye Da Siyarwa 

Ganduje Ya Nada Baffa A Matsayin Shugaban Hukumar Kare Hakkin Masu Siye Da Siyarwa 

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso  Ne Kaɗai Ɗan Siyasar Da Zai Iya Maye Gurbin Buhari — Jigo A NNPP

Kwankwaso  Ne Kaɗai Ɗan Siyasar Da Zai Iya Maye Gurbin Buhari — Jigo A NNPP

July 22, 2025
Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar

Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar

July 22, 2025
Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO

Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO

July 22, 2025
Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu

Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu

July 22, 2025
Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

July 22, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Shawarwari Da Tattaunawa

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Shawarwari Da Tattaunawa

July 22, 2025
Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaddamar Da Kwaskwarimar Majalisar Dokoki Kan Naira Biliyan 7

Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaddamar Da Kwaskwarimar Majalisar Dokoki Kan Naira Biliyan 7

July 22, 2025
Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu

Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu

July 22, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

July 22, 2025
Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi

Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi

July 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.