• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Sanda Sun Kashe Dan Bindiga, Sun Kwato AK-47 A Zamfara

bySadiq
3 years ago
'Yan Bindiga

Jami’an ‘yan sanda a Jihar Zamfara sun kashe wani dan bindiga tare da kwato bindiga kirar AK 47 da alburusai 18 a wani artabu da suka yi a kauyukan Saran Gamawa da Anguwar Mata da ke Karamar Hukumar Gummi a Jihar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin  rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara, SP Muhammad Shehu, ya fitar a Gusau ranar a Litinin.

  • Za A Shafe Shekaru Kafin A Kawo Karshen Yakin Ukraine Da Rasha —NATO
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Coci, Sun Kashe Mutane 3 A Kaduna

“A ranar 19 ga Yuni, 2022, jami’an ‘yan sandan da aka tura ta hanyar Gummi/Bukkuyum, sun samu kiran gaggawa cewa, ‘yan ta’adda dauke da makamai a kan babura sun kai farmaki Saran Gamawa da kauyukan Unguwar Mata da ke makwabtaka da su da nufin sace mutanen da ba su ji ba ba su gani ba.

“Rundunar ‘yan sanda tare da hadin gwiwar ‘yan banga na kauyukan da lamarin ya shafa, sun hada karfi da karfe tare wajen yakar ‘yan ta’addan a wani kazamin artabu da aka dauki tsawon sa’o’i ana yi.

“Sakamakon haka, daya daga cikin ‘yan ta’addan ya samu munanan raunuka, an samu bindiga kirar Ak 47 a wajen dan bindigar, yayin da wasu da dama suka tsere cikin dajin da raunukan harbin bindiga daban-daban,” in ji Shehu.

LABARAI MASU NASABA

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Ayuba Elkanah, ya yaba da jajircewar da ‘yan sandan suka yi, ya kuma bukace su da kada su yi kasa a gwiwa wajen ganin rundunar ta kare rayuka da dukiyoyin mutanen da ba su ji ba ba su gani ba a jihar.

Elkanah ya kuma umarci Kwamandan yankin Anka da DPO da ke makwabtaka da su tura tawagar hadin gwiwa don ci gaba da sintiri don dakile ci gaba da kai hare-hare a kan al’ummomin da ke yankunan.

Ya ce rundunar ta kuma tura domin ceto mutanen biyu da maharan suka yi garkuwa da su kafin isowar ‘yan sanda.

“Yayin da yake tabbatar da kudurin rundunar na kare rayuka da dukiyoyi a jihar, ya yi kira ga jama’a da su ba ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro hadin kai a kokarin kawar da ‘yan bindiga a jihar,” in ji kakakin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba
Labarai

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci
Labarai

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Next Post
Ganduje Ya Nada Baffa A Matsayin Shugaban Hukumar Kare Hakkin Masu Siye Da Siyarwa 

Ganduje Ya Nada Baffa A Matsayin Shugaban Hukumar Kare Hakkin Masu Siye Da Siyarwa 

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version