Rundunar ’Yansandan Jihar Katsina ta dakile wani harin ’yan bindiga a ƙaramar hukumar Dutsin-Ma, tare da ceto mutane huɗu da aka yi garkuwa da su, ciki har da jaririn da ake shayarwa.
Lamarin ya faru ne da sanyin safiyar Laraba, bayan rundunar ta samu kiran gaggawa cewa wasu ’yan bindiga sun yi garkuwa da mata uku a ƙauyen Makwanta.
Jami’an ’yansanda sun bi sawun maharan har zuwa iyakar Dutsin-Ma da Danmusa, inda suka yi musayar wuta mai tsanani da su.
Rundunar ta ce ’yan bindigar sun tsere zuwa cikin daji bayan jami’an sun yi galaba a kansu da ƙarfin wuta, inda ake zargin wasu daga cikinsu sun samu raunukan harbin bindiga. Sun kuma bar mutanen huɗu da suka yi garkuwa da su, waɗanda aka ceto ba tare da wani rauni ba.
Daga cikin kayayyakin da jami’an suka kwato akwai bindigar AK-47 guda ɗaya mai harsasai biyar, wayar Tecno, na’urorin MP3 guda uku, wuƙa da kuma kunshin busassun ganyaye guda uku da ake zargin tabar wiwi ce.
Kwamishinan ’Yansandan jihar, CP Ali Umar Fage, ya yaba wa jami’an da suka gudanar da aikin bisa jarumtakarsu, ƙwarewa da kuma gaggawar da suka nuna wajen tunkarar harin.
Ya tabbatar da aniyar rundunar na ƙara tsaurara yaƙi da ’yan bindiga da sauran miyagun laifuka a faɗin Jihar Katsina.













