Tsohuwar uwargidan Shugaban Nijeriya, Aisha Buhari, ta ziyarci tsohon Mataimakin Shugaban ƙasa, Atiku Abubakar.
Atiku ne ya bayyana hakan a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X ranar Laraba, inda ya bayyana ganawar da Aisha Buhari a matsayin abin yabawa.
Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya ce ziyarar ta kuma jaddada muhimmancin waɗanda ke neman inganta Nijeriya su mayar da hankali kan inganta walwalar ’yan ƙasa da kuma makomarsu.
Atiku ya ce iyalai a faɗin ƙasar na fuskantar ƙarin matsin tattalin arziƙi sakamakon tashin farashin kayayyakin masarufi da suka hada da abinci, sufuri, ilimi da kiwon lafiya.
Ya ce irin wannan yanayi na buƙatar a fifita jin daɗin jama’a da samar da kyakkyawar makoma ga ’yan Nijeriya.













